Abdul Tech Systems Ltd
Labarai

An Kona Dillalan Kwaya 3 Da Ransu A Afrika Ta Kudu

Published by Zainab Sabitu

Ƴan sanda a Afrika Ta Kudu sun ce suna cikin halin ko-ta-kwana bayan wani lamari da ya faru inda aka ƙona wasu mutum uku da ransu a cikin gida.

Rahotanni sun ce jama’ar gari ne suka ƙona mutanen bisa zarginsu da safara da dillancin miyagun ƙwayoyi.

Waɗanda ake zargin suna tsakanin shekarun 22 ne zuwa 36, kamar yadda ƴan sandan ƙasar suka bayyana.

Waɗanda aka ƙona ɗin an ce sun caka wuƙa da kuma raunata waɗanda suka kai musu harin, amma an tura su cikin gida inda aka cinna wa gidan wuta suka ƙone a ciki.

Babu wanda aka kama kan wannan lamari.

🤞 Don’t miss any Article!

We don’t spam! Read more in our Privacy Policy.

Oh hi there 👋
Don't miss anything.

Sign up to receive awesome content in your inbox.

We don’t spam! Read our Privacy Policy for more info.

About the author

Zainab Sabitu

I'm who I am and that's just enough.
I'm definitely the best of my kind.
Just take a seat and grab a cookie.

Leave a Comment