Abdul Tech Systems Ltd
Labarai News

Hadarin Mota Ya Kashe Mutum 12 A Jihar Kwara

Published by Kamaluddeen Ibrahim

Akalla mutum 12 ne suka mutu a wani hatsarin mota da ya faru a kan hanyar Ilorin zuwa Ogbomosho da ke Jihar Kwara a ranar Asabar.

Aminiya ta rawaito cewa wata mota kirar Toyota Hiace mai cin mutum 18 da ke hanyar zuwa Legas ce ta yi taho-mu-gama da wata babbar mota kirar Daf.

Fasinjoji shida dai da suka tsira da ransu sun ji raunuka daban-daban a hatsarin da ya faru wajen misalin karfe 7:00 na safe.

Wani ganau ya ce hatsarin ya faru ne lokacin da direban Hiace din yake tsala gudu a hannun da ba nasa ba.

Kwamandan Shiyya na Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) reshen Jihar ta Kwara, Jonathan Owoade, ya tabbatar wa wakilinmu faruwar hatsarin.

🤞 Don’t miss any Article!

We don’t spam! Read more in our Privacy Policy.

Oh hi there 👋
Don't miss anything.

Sign up to receive awesome content in your inbox.

We don’t spam! Read our Privacy Policy for more info.

About the author

Kamaluddeen Ibrahim

Publisher/Editor at Albarka Radio.

Leave a Comment