Labarai

Kwanaki 3 Za’ayi Ana Ruwa Da Tsawa A Najeriya —NiMet

Hukumar Kula da Yanayi ta Kasa (NiMet) ta yi hasashen za a yi ruwan sama da tsawa daga ranar Juma’a zuwa Lahadi a fadin kasar.

Hasahen yanayin NiMet ta fitar ranar Alhamis a Abuja ya nuna za a yi tsawa a sassan jihohin Sakkwato, Zamfara, Kebbi, Yobe, Borno, Taraba da Adamawa da safiyar Juma’a.

Akwai kuma yiwuwar yin tsawa a sassan jihohin Jigawa da Kaduna da Bauchi da Gombe da Kano da Katsina.

Hukumar ta yi hasashen za a samu ruwan sama na jef-jefi a yankin Arewa ta tsakiya a duk tsawon kwanaki ukun.

NiMet ta yi hasashen samun ruwan sama mai tsananin gaske na tsawon sa’o’i a Kudu da safe tare da matsakaicin ruwan sama a yankin gabar teku daga baya da rana.

“A ranar Asabar, ana sa ran girgije ya mamaye yankin Arewa tare da tsawa a sassan jihohin Kano, Katsina da Sakkwato da safe.

“Washegari, ana sa ran za a yi tsawa a sassan jihohin Kano da Bauchi da Kebbi da Katsina da kuma Sakkwato.

“Ana sa ran yankin Arewa ta tsakiya zai kasance cikin gajimare tare da yiwuwar samun ruwan sama a sassan jihohin Kwara da Neja da kuma Babban Birnin Tarayya,” a cewar rahoton.

Hukumar ta kuma bayyana cewa ana sa ran samun ruwan sama a sassan babban birnin tarayya da jihoihn Binuwai da Kogi da Filato da da rana da kuma yamma.

Ta kuma yi hasashen yanayi mai hadari gami da yiwuwar samun ruwan sama a johin Ribasa da Akwa Ibom da safe.

Za kuma a yi ruwan sama matsakaici a sassan jhohin Ekiti da Ondo da Ogun da Oyo da Osun da Enugu da Imo da Edo.

Hukumar ta yi hasashen yanayi na cida a yankin Arewa a ranar Lahadi da yiwuwar tsawa a sassan jihohin Kebbi da Borno da Sokoto da safe.

An yi hasashen za a yi tsawa a sassan jihohin Sokoto da Kano da Bauchi da Gombe da Borno da Adamawa da rana da yamma.

“Ana sa ran yankin Arewa ta tsakiya zai kasance da gajimare da safe. Ana sa ran za a yi tsawa a sassan jihohin Filato da Benue da rana da yamma.

“Ana sa ran za a yi gajimare da gajimare a biranen kudancin Kudancin kasar.

“Da rana, ana sa ran ruwan sama matsakaici a sassan jihohin Ogun da Imo da Edo da Delta da Legas da Bayelsa da Kuros Riba da Akwa Ibom,” in ji shi.

A cewar hukumar, har yanzu sassan Arewacin Najeriya na cikin hadarin ambaliya.

Don haka ta shawarci hukumomin gaggawa za su kasance cikin shiri.

Hukumar ta kuma shawarci kamfanonin jiragen sama da su sami sabbin rahotannin yanayi daga NiMet don ingantaccen shiri a ayyukansu.

 

Leave a Reply