Labarai

Nan Da Disamba Za Mu Kawo Karshen Ayyukan Ta’addanci —Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce daga yanzu zuwa wata hudu masu zuwa za ta kawar da ayyukan ta’addanci a Najeriya.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola, shi ne wanda ya ba da tabbacin a lokacin jawabin hadin gwiwan kan tsaro tare da Ministan Tsaro da na Harkokin ’Yan Sanda.

Aregbesola ya ce: “Muna bai wa ’yan Najeriya tabbacin isashen tsaro da aminci, shi ya sa shugaban kasa ya umarce mu da mu sanar da ku cewa daga yanzu zuwa watan Disamba, kullun tsaro da aminci da za ku samu za su inganta.

“Abin da muke fama da shi yanzu ba wani abu ba ne face harin matsorata da aka tarwatsa maboyansu a wurare daban-daban, wanda suna yin haka ne domin a rika ganin cewa har yanzu da sauran karfinsu.

“Babbar manufarmu ita ce kawar da su gaba daya kasa sannan mu dawo da aminci a kowane taki na fadin kasar nan; kuma da izinin Allah hakan zai samu zuwa watan Disamba na wannan shekara.

“Za a ga da kamar wuya amma zai yiwu, domin mun shirya domin tabbatar da aminci da tsaro a kowane taki a fadin kasar Najeriya, kuma tuni aka bayar da umarnin yin hakan,” in ji Aregbesola.

A cewar ministan, bullar annobar COVID-19 na daga cikin abubuwan da suka kara dagula matsalar tsaro a Najeriya, duk kuwa da matakan da Gwamnatin Tarayya ta dauka.

“Amma za mu ci gaba da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’ar Najeriya da kuma baki, domin tabbatar da aminci da kuma murkushe bata-gari da ke barazana ga al’umma a fadin kasarmu,” in ji shi.

Ta ci gaba da cewa, “Ba za mu huta ba har sai an samu cikakken aminci a Najeriya.”

Leave a Reply