Labarai News

Hadarin Mota Ya Kashe Mutum 12 A Jihar Kwara

Published by Kamaluddeen Ibrahim

Akalla mutum 12 ne suka mutu a wani hatsarin mota da ya faru a kan hanyar Ilorin zuwa Ogbomosho da ke Jihar Kwara a ranar Asabar.

Aminiya ta rawaito cewa wata mota kirar Toyota Hiace mai cin mutum 18 da ke hanyar zuwa Legas ce ta yi taho-mu-gama da wata babbar mota kirar Daf.

Fasinjoji shida dai da suka tsira da ransu sun ji raunuka daban-daban a hatsarin da ya faru wajen misalin karfe 7:00 na safe.

Wani ganau ya ce hatsarin ya faru ne lokacin da direban Hiace din yake tsala gudu a hannun da ba nasa ba.

Kwamandan Shiyya na Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) reshen Jihar ta Kwara, Jonathan Owoade, ya tabbatar wa wakilinmu faruwar hatsarin.

About the author

Kamaluddeen Ibrahim

Leave a Comment