Labarai

Zulum Ya Ziyarci Iyalan Masu Kamun Kifi Da Yan Ta’ada Su Ka Hallaka A Borno

Published by Kamaluddeen Ibrahim

Gwamana Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya ziyarci iyalan masu kamun kifi guda 30 wadan da yan ta’addan Boko Haram suka hallaka a ranar laraban nan a kauyen Muldolo wanda ke karamar hukumar Ngala na jihar.

Gwamna Zulum ya kasance a yankin Dikwa inda masu kamun kifin suke zaune sukan kumayi sana’ar kamun kifi ne a yankin Mukdolo kafin daga bisani akayi musu kwantan Bauna.

Gwamnan ya gana da dukkanin iyalan masu kamun kifin a fadar Shehun Dikwa Alhaji Ibrahim Ibn Ibrahim El-Kanemi.

Karanta: APC Ta Bukaci Ganawa Da Tinubu, Kashim, Sanatoci, Yan Majalisan Wakilai

Yace a madadin gwamnati da kuma al’umar gari , ya mika sakon ta’aziyyarsa wa iyalai da yan uwan da abin ya shafa , Yakuma bukace su dasu maida komai zuwa ga Allah , yace shi kadai zai iya yin hisabi a gidan duniya dakuma ranar gobe.

Gwamna Zulum Yakuma gabatar da kayayyakin tallafi wa kowanni iyalan da suka rasa yan uwansu, Yakuma tabbatar musu da cewa zai cigaba da tallafa musu a kowanni lokaci.

Shima a nasa bangare Shehun Dikwa ya mika sakon godiyarsa wa gwamna Zulum amadadin al’umar yankin Yakuma yi addu’ar Allah ya basu hakuri Yakuma saka masa da Alkhairi.

About the author

Kamaluddeen Ibrahim

Leave a Comment