Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Atiku ya bukaci Kotun koli tayi watsi da bukatar Tinubu kan takardun bogi

October 19, 2023 2 minutes read

 

Dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bukaci Kotun Koli ta yi watsi da bukatar Shugaba Tinubu na kin karbar sabbin hujjojin Atikun kan zargin Tinubun da amfani da takardun bogi.

Atiku ya gabatar da sabbin hujjoji ga Kotun Kolin kan zargin amfani da takardun bogi da yake cewa Tinubu ya gabatar wa Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu da Tinubun ya lashe.

Ya ce amfani da takardun bogin da Tinubu ya yi domin rike matsayi mafi girma a Najeriya na da matukar hatsari bisa tanadin kundin tsarin mulkin Najeriya, don haka ya kamata a taka masa burki.

A kan haka ne ya nemi Kotun Kolin da ta yi watsi da bukatar Tinubu na kin karbar sabbin hujjojin bisa hujjar sarkakinar da za su haifar a shari’ar.

Lauyan Tinubu, Wole Olanipekun (SAN) ya shaida wa kotun cewa maganar takardun shaidar karatu batu ne da ya danganci abubuwan kafin zabe, don kotun ba ta da hurumin karbar sabbin hujjoji a kansu.

Amma lauyan Atiku, Chris Uche (SAN)  ya bayyana cewa rashin karbar hujjojin ne zai haifar da karin sarkakiya, don haka ya ce karbar karin hujjojin zai tabbatar da cikakken adalci a shari’ar, “don gano gaskiyar zargin amfani da takardun bogin ko akasin haka.”
Jaridar Aminiya
Tags: APC Atiku Abubakar Bola Ahmed Tinubu PDP Takardun bogi

Post navigation

Previous: ACReSAL organises Workshop on Gender Based Violence for stakeholders in Bauchi
Next: Kwamandan Boko Haram, Bulama Bukar ya miƙa wuya ga sojin Najeriya 

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.