Skip to content
September 20, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Hayar Lauyan Tinubu Ya Wakilci Shari’arsa A Kotu

October 7, 2023 2 minutes read

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dauki hayar fitaccen lauyan nan, Cif Wole Olanipekun (SAN) domin ya wakilci shari’arsa a Kotun Daukaka Kara.

Aminiya ta ruwaito cewa a watan da ya gabata ne Kotun Sauraron Karar Zabe ta Jihar Kano ta sauke Abba Kabir Yusuf a matsayin gwamnan jihar, inda ta ayyana Nasir Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya yi nasara a zaben da aka gudanar ranar 18 ga watan Maris.

Da yake kalubalantar hukuncin kotun, Abba Kabir Yusuf ya gabatar da korafi a gaban Kotun Daukaka Kara da hujjoji har guda 42, inda ya bukaci kotun ta yi watsi da hukuncin sannan kuma ta yi watsi da karar da APC ta shigar.

A kunshin karar da Abba Kabir Yusuf ya shigar, Aminiya ta lura cewa, Cif Wole Olanipekun (SAN), wanda ya jagoranci lauyoyin da su ka kare Shugaba Bola Tinubu a shari’ar zaben Shugaban Kasa tsakaninsa da Atiku Abubakar da Peter Obi, shi ne zai wakilci tasa shari’ar.

Haka kuma, a cikin tawagar lauyoyin Gwamna Abba akwai; Bode Olanipekun (SAN) da Ibrahim G. Waru da Akintola Makinde, yayin da Cif E.O.B. Offiong zai ci gaba da kasancewa lauyan na APC.

Jaridar Aminiya

Tags: Abba Kabir Yusuf APC NNPP Shugaba Bola Ahmed Tinubu

Post navigation

Previous: Wata Mata ta yi kashin fasassun kwalabe a Kalaba
Next: Ƴan Sanda Sun Kama Kananan Yara Da Laifin Fashi Da Makami A Delta

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.