Labarai

Tinubu da Shettima sun sha rantsuwar kama aiki

Tsohon gwamnan jihar Lagos, Sanata Bola Ahmad Tinubu ya yi rantsuwar kama aiki a matsayin sabon shugaban ƙasar Najeriya.

Ya kasance shugaban kasa na goma sha shida a jerin shugabannin ƙasar.

Ya yi alkawarin yin biyayya a kundin mulkin Najeriya tare da yin aiki ba tare da nuna son zuciya ba.

Tinubu ya sanya hannu a takardar rantsuwar kama aiki.

Tsohon gwanan jihar Borno, Sanata Kashim Shettima ya yi rantsuwar kama aiki a mastayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Najeriya.

Ya yi alkawarin yin biyayya ga kundin tsarin mulkin Najeriya tare da yin aiki ba tare da nuna son zuciya ba.

Shettima ya sanya hannu a takardar rantsuwar kafin daga bisani ya koma wurin zamansa.

About the author

Muhammad Sani Abdulhamid

Leave a Comment