Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • News

NOA Ta Yaba wa EFCC Kan Yaki da Laifukan Intanet

August 25, 2025 (Last updated: August 25, 2025) 2 minutes read

Daga Ude Ogbonnaya Israel

Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Kasa (NOA) ta yaba wa Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) bisa nasarar da ta samu a kwanan nan wajen rusa wani gungun masu aikata laifukan intanet da ke aiki a ƙasar nan.

NOA ta bayyana cewa wannan nasara ta nuna gagarumar alama cewa Najeriya ba za ta lamunci kowanne irin laifi ba, ba tare da la’akari da kasar da masu aikata laifin suka fito ba.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Sadarwa da Hulɗa da Jama’a na hukumar NOA, Bala Musa, ya fitar, hukumar ta bayyana cewa Najeriya a matsayinta na ƙasa mai cin gashin kanta da tsayuwa akan doka, tana da nauyin kare mutuncinta da martabarta a idon duniya.

Musa ya bayyana cewa ko da yake NOA na ci gaba da wayar da kai kan ɗabi’a ta gari da kuma alhakin zama ɗan ƙasa nagari ta hanyar nuna muhimmancin riko da martabar a ci gaba da gangamin wayar da kan jama’a da take yi, yana da matuƙar muhimmanci ga ’yan Najeriya da ma baƙi su girmama dokokin ƙasar tare da guje wa duk wani aiki da zai iya cutar da tsaron kasa ko kuma tauye darajar al’uma.

“Masu aikata laifukan intanet, ko su ’yan ƙasa ne ko kuma baƙi, dole su gane cewa hukumomin tsaro na cikin shiri, na da kayan aiki, kuma suna da ƙuduri wajen kamo duk wanda ya aikata laifi. Najeriya ba za ta zama mafaka ko wurin gudanar da mugayen ayyuka ba,” in ji sanarwar.

Ya ƙara da kiran shugabanni, sarakunan gargajiya, cibiyoyin ilimi, ƙungiyoyin fararen hula da kuma kafafen yada labarai da su ci gaba da yaɗa bayane kan riko da darajar Najeriya, kishin ƙasa da ɗaukar nauyin ci gaban ƙasa.

Musa ya kara da cewa; “muna yabawa EFCC bida wannan jajircewa da suka nuna. Ta haka ne kasashe ke ginuwa – ta hanyar daukar tsauraran matakai wajen tabbatar da bin doka da oda”.

Tags: EFCC Federal Government of Nigeria National Orientation Agency President Bola Ahmed Tinubu

Post navigation

Previous: NUJ Bauchi Sympathizes with Albarka Radio Over Technical Breakdown
Next: Bauchi sensitizes stakeholders on HOPE Programme

Related Stories

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.