By Muhammad Sani Muazu
Kungiyar Malaman Kwalejojin Kimiyya Fasaha a Najeriya (ASUP) ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin kwanaki 21 domin warware muhimman matsalolin da ta ce suna barazana ga makomar ilimin kwalejojin kimiyya da fasaha a ƙasar nan.
Shugaban kungiyar na shiyyar B, Lumpye Innocent Simji ne, ya bayyana hakan a taron manema labarai da kungiyar ta gudanar a Bauchi a ranar Juma’a, inda ya ce an yanke wannan shawarar ne bayan taron gaggawa na majalisar zartarwar ƙasa ta kungiyar (NEC) da aka gudanar a Abuja a ranar 14 ga watan Agusta, na shekarar 2025. Ya yi gargadin cewa idan gwamnati ta yi biris, kungiyar ba za ta yi wata-wata ba wajen shiga yajin aiki a fadin kasar nan.
Daga cikin matsalolin da ASUP ta lissafa har da rashin sakin takardar umarni daga Hukumar Albashi ta Kasa (NSIWC) domin biyan “alawus alawus din karantarwa”, rashin biyan bashin karin albashin kashi 25/35 cikin 100, da kuma gazawar wasu gwamnatocin jihohi wajen aiwatar da sabon tsarin albashi da mafi ƙarancin albashi na kasa.
Sauran bukatun sun haɗa da jinkirin amincewa da tsarin da zai kawar da wariyar da ake yi tsakanin masu digiri da masu takardar HND, rashin sakin kudaden tallafi na NEEDS Assessment da aka amince da su don ci gaban gine-gine, matsalar kwace aikin tabbatar da inganci daga hukumar NBTE zuwa hannun masu zaman kansu da ba su cancanta ba, da kuma rashin kafa hukumar da za ta kula da bangaren kwalejojin kimiyya da fasaha kai tsaye.
Kungiyar ta kuma yi korafi kan jinkirin biyan kudaden karin matsayi na malamai tun daga shekarar 2019, rashin kammala tattaunawar sabunta yarjejeniyar kungiyar ASUP da gwamnatin tarayya na shekarar 2010, da kuma kin aiwatar da wasu sassa na dokar kwalejojin kimiyya da fasaha ta Tarayya a cikin kwalejojin jihohi. Haka kuma ta koka kan ci gaba da wariyar da ake yi wa masu HND a cikin aikin gwamnati da kuma rashin kammala tattaunawa kan biyan bashin matakin albashi na CONTISS 15.
ASUP ta yi tir da abin da ta kira karfi a harabar Kwalejin kimiyya da Fasaha ta Tarayya, da ke Nekede, inda ake zargin ana tura jami’an tsaro dauke da makamai domin hana ayyukan kungiyar. Kungiyar ta zargi Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da rashin daukar mataki kan wannan lamarin.
Simji ya ce rashin son tattaunawa da gaskiya daga bangaren Ma’aikatar Ilimi ya bar kungiyar da zabi guda – na bayar da wa’adin kwanaki 21. Ya gargadi cewa idan ba a dauki matakin gaggawa ba, ASUP za ta shiga yajin aiki tare da dakatar da dukkanin ayyukan koyarwa a kwalejojin kimiyya da fasaha na gwamnati a fadin kasa.

Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.









