Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Ƴan sanda sun kama wata Mata Da Ta Sace ƴar Shekara 3 A Neja

November 13, 2023 (Last updated: November 13, 2023) 1 minute read

 

’Yan sandan sun kama wata mata mai shekara 51 kan zargin satar wata yarinya ’yar shekara uku a garin Minna na Jihar Neja.

Da yake gabatar da wadda ake zargin, kakakin ’yan sandan jihar, DSP Wasiu Abiodun, ya ce a ranar 25 ga watan Oktoba 2023 aka gan ta a “unguwar Keteren-Gwari tana kokarin shiga motar haya domin tafiya da wata yarinya ’yar shekara uku da ake zargin an sace ta.”

Ya ce ‘yan sanda da ke aiki a yankin Tudun-Wada sun kama wadda ake zargin tare da yarinyar kuma da suka yi mata tambayoyi, ta amsa cewar ta sato yarinyar ce daga wani gida a unguwar Tudun-Natsira a ranar da misalin karfe 8 na dare.

Ta kara da cewa ta yi niyyar sayar da ita ga wata mata a garin Nnewi da ke Jihar Anambra, wadda ta ba ta kwangilar a kan kudi N530,000.

Ta ce ta karbi wasu daga cikin kudin N230,000 kafin ta kawo yarinyar da ta sace.

Abiodun, ya ce an mayar da yarinyar ga iyayenta kuma ana ci gaba da kokarin cafke daya matar da ke Anambra.

Tags: 'Yan Sanda Neja Satar yara

Post navigation

Previous: Just In: Boat Carrying Electoral Officers, Materials Capsizes In Bayelsa State
Next: Bauchi NSE justifies ₦10.3bn spent on 11km dual carriageway

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.