Home Labarai Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani...

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

Daga Zainab Faruk

Fiye da mata dari ne suka kammala samun horo kan fasahar sadarwa ta zamani a jihar Bauchi, karkashin wata hadin gwiwa tsakanin Hukumar Raya Fasahar Sadarwa ta Zamani (NITDA) da shirin Renewed Hope Initiative (RHI), a wani shiri da nufin ƙarfafa mata da ilimin zamani.

An gudanar da bikin kammala horon ne a Cibiyar Raya Ilimi ta Jihar Bauchi (Education Resource Centre), karkashin taken “Mata da Fasahar Zamani.” Horon ya gudana a Cibiyar Fasahar Sadarwar Zamani ta Justice Zainab Adamu Bulkachuwa, wanda NITDA ta gina tare da mika ta ga gwamnatin jihar Bauchi don ci gaban mata a fannin ilimin zamani.

A jawabinta na bude taron, Uwargidar Gwamnan Jihar Bauchi, Hajiya Aishatu Bala Abdulkadir Muhammad, wadda ita ce jagorar shirin a jihar, ta yaba da jajircewar matan da suka halarci horon, tana mai cewa horar da mace a bangaren zamani tamkar bude mata kofar cigaba ne.

“Yau rana ce ta musamman. Muna taya wadannan mata murna bisa nasarar da suka samu na kammala horo a bangaren fasahar zamani. Ilimin da kuka samu zai taimaka muku wajen habaka kasuwanci, taimakawa ‘ya’yanku da kuma kara samun ’yancin kai,” in ji ta.

n

Uwargidan Gwamna ta ce makarantar da aka gudanar da horon, wato Cibiyar Fasahar Zamani ta Justice Zainab Adamu Bulkachuwa, ta zama wata muhimmiyar kafa ta ilimi da ci gaban mata a jihar Bauchi. Ta kuma yaba da irin gudummawar da NITDA ta bayar wajen samar da cibiyar, da kuma hadin kan da Renewed Hope Initiative ta nuna a cikin aikin.

A cewarta, “A yau duniya na tafiya ne bisa ilimin zamani. Wanda bai san yadda ake amfani da kwamfuta da intanet ba tamkar wanda bai iya karatu ba ne. Yana da matukar muhimmanci mata su samu wannan dama.”

Ta bukaci matan da suka kammala horon da su yi amfani da wannan damar wajen:

Fara sana’o’in kan intanet

Tallafawa yara da karatu

Koyar da sauran mata

Zama masu dogaro da kai

Haka kuma, Uwargidar Gwamnan ta bukaci su ci gaba da koyon sabbin abubuwa saboda duniya tana canzawa cikin sauri, tare da rike zumunci da abokan karatu domin taimaka wa juna a fannin cigaban kasuwanci da rayuwa.

A jawabin sa na fatan alheri, Babban Sakataren Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Bauchi, Dr. Ali Babayo, wanda ya wakilci Kwamishinan Ilimi, Dr. Muhammad Lawal Rimin Zayam, ya bayyana cewa cibiyar horon Kan Fasahar Sadarwar Zamani ta Justice Zainab ta kasance cikin halin tabarbarewa kafin zuwan Gwamna Bala Muhammad, amma yanzu ta zama cibiyar da ke da tsari irin na kasa da kasa.

“Gwamnan Bauchi ya taka rawar gani wajen kawo sauyi a wannan cibiya. Tare da goyon bayan uwargidansa, wannan katafaren aiki ya tabbata. Muna godiya,” in ji shi.

Ya kuma bukaci hadin kan kungiyoyi masu zaman kansu da masu hannu da shuni da su mara wa kokarin gwamnati baya wajen samar da ilimi ga mata da matasa.

Haka kuma, Kwamishinar Harkokin Mata da Ci gaban Yara, Hajiya Zainab Babantakko, ta yaba wa Hajiya Aishatu Bala Abdulkadir Muhammad bisa goyon bayanta marar yankewa ga mata, tana mai bayyana ta a matsayin uwa ta hakika ga mata na jihar Bauchi.

“Mama, ke ba wai uwace a baki ba ce, amma uwace a aikace. Kina da zuciyar taimako, koda yaushe kina bude kofa ga mata da ke cikin bukata. Allah ya saka miki da alkhairi,” in ji ta.

Ta kuma bukaci matan da suka samu horon da su daina dogaro da taimako kawai, su zama masu bada gudunmawa ga cigaban kansu da al’ummarsu.

Matan da suka amfana da horon sun samu kwarewa a fannonin kamar: amfani da manhajar WhatsApp don kasuwanci, amfani da bankin wayar salula cikin tsaro, koyon yadda ake ciniki a intanet da kuma fahimtar yadda ake samun jagora (mentorship).

Yayin da aka raba takardun kammala horon, an jaddada cewa wannan horo wani sabon mataki ne na ciyar da matan Bauchi gaba a duniyar zamani.

Sako daya ne daga bikin: Matan Bauchi sun tashi tsaye don karɓar ilimin zamani – yanzu lokaci ne na aiwatar da shi.


Discover more from Albarka Radio

Subscribe to get the latest posts sent to your email.