Skip to content
September 20, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Ƴan bindiga sun kashe mutane da dama, sunyi garkuwa da wasu a Kano

October 16, 2023 2 minutes read

 

Ana fargabar cewa wasu ’yan bindiga sun kwashe wani adadi da jama’ar kauyen Yola da ke Karamar Hukumar Karaye a Jihar Kano.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, lamarin na zuwa ne bayan wasu ’yan bindiga da ake zargin ’yan daban daji sun kai hare-hare a yankuna daban-daban na kauyen.

Bayanai sun ce hare-haren da aka kai yankuna daban-daban sun yi sanadiyyar mutuwar jama’a da dama yayin da aka yi garkuwa da wasu.

A cewar wani mazaunin kauyen da ya bukaci a sakaya sunansa, hare-haren sun auku a yankuna daban-daban na kauyen da ba zai iya fayyace adadin mutanen da aka kashe ko aka yi garkuwa da su ba.

“Na samu labarin cewa a rana ta farko sun sace mutum huud sannan sun kashe wasu mutum biyu.

“Haka kuma a rana ta biyu sun kashe karin wasu mutum biyu tare da garkuwa da mutum daya.

“Sai dai ba ni da tabbaci kan alkaluman mutanen da aka sace ko aka kashe.

“Amma ba na tantamar cewa an dauke wasu mutane kuma an kashe wasu.

“Abin da ya fi muhimmanci a yanzu shi ne Karaye tana bukatar dakarun soji su kawo mana dauki saboda wadannan hare-hare,” a cewarsa.

Rahotanni sun bayyana cewa, a bayan nan yankunan Karamar Hukumar Karaye da Rogo na fuskantar matsalolin tsaro saboda kusancinsu da Jihohin Kaduna da Katsina.

Ana iya tuna cewa, a watan Afrilun da ya gabata ne wasu ’yan daban daji suka kashe wani mutum daya tare yin garkuwa da wani dan kasuwa a Kauyen Gangarbi da ke Karamar Hukumar Rogo, Alhaji Nasiru Na’ayya.

Kazalika, a shekarar 2021 ce Masarautar Karaye ta yi koken yadda ake samun kwararowar masu hakar ma’adanai daga Jihar Zamfara.

Wasu majiyoyi sun ce tuni masarautar ta dauki matakam da suka dace domin yi wa tufkar hanci.

Sai dai ƙoƙarin da wakilinmu ya yi domin jin ta bakin mai magana da yawun da rundunar ’yan sandan Jihar Kano, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ci tura a yayin da bai amsa kiran wayarsa ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Jaridar Aminiya

Tags: Kano Karaye ƴan bindiga

Post navigation

Previous: Digital Skills: FG opens portal for eligible Nigerians
Next: Ministan Tsaro Da Sakataren Gwamnatin Chadi Sun Ajiye Aikinsu kan Bidiyon Batsa

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.