Skip to content
September 14, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

An kulle Masallacin Jumma’a kan rikicin limancin a Lagos

September 25, 2023 2 minutes read

 

An samu rashin jituwa akan mukamin babban liman a Masallacin Epe da ke a jihar Legas, inda daya daga cikin rassan Masallacin da ke a jihar limamai biyu suke yi ikirarin su ne manyan limaman Masallacin.

Rashin jituwar wadda ta kunno kai a lokacin Sallar Juma’ar da ta gabata, lamarin ya faru ne a yayin da limaman biyu, suka yi yinkurin jagoranrar Sallar ta Juma’a wanda hakan ya janyo cacar baki da wuce gona da iri.

Babban Masallacin wanda ke a yankin Opo, rashin jituwar ya janyo mataimakin Sifeta Janar na ‘yansansa na shiyya ta biyu ya bayar da umarni a kulle Masallacin har sai an lalubo da mafita kan rikicin.

A cikin wani faifan bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta na zamani, ya nuna yadda jami’an ‘yansanda suka yi awon gaba da babban limamin Masallacin, Alhaji Abdullateef Oladapo.

Hakan ya biyo bayan yadda limaman Masallacin biyu suka kasance a cikin Masallacin a lokacin Sallar ta Juma’a, ciki har da Alhaji Abdulkabir Oriyomi wanda ya nuna son jagorantar Sallar ta ranar Juma’a 22 ga watan Satumbar 2023.

Kazalika, an ruwaito cewa, gwamnatin jihar ta karkashin ofishin mataimakin gwamnan jihar Dakta Obafemi Hamzat, ya tura jami’an ‘yansansa zuwa Masallacin don su tabbatar da bin doka da oda.

An ruwaito cewa, an nada Oladapo a matayin babban limamin Masallacin ne biyo bayan wata takardama a shekarar 2012 wadda ta yi sanadiyyar aka mayar da Oriyomi zuwa wani Masallacin da ke a gundumar Epe.

Jaridar Leadership

Tags: Epe lagos masallacin juma'a Rikici

Post navigation

Previous: Tinubu Ya Ciwo Bashin Tiriliyan 1.6 Daga Bankin Duniya A Cikin Wata 4
Next: Mun nemi ƙarin bayani daga Gwamnatin Tarayya kan zaman sirri na sulhu da wasu jami’anta suke jagoranta a Zamfara – Dauda

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.