Skip to content
September 20, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Dalilin da ya sa Buhari ke rayuwar nadama a yanzu – Solomon Dalung

October 8, 2023 2 minutes read

 

Tsohon Ministan Wasanni da Ci gaban Matasa, Solomon Dalung, ya yi ikirarin cewa a halin yanzu tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari yana rayuwar nadama kan yadda makusantansa suka bata masa suna a lokacin shugabancinsa.

Dalung wanda ya yi aiki a gwamnatin Buhari, ya ce gwamnatin ta gaza wajen cika alkawuran da ta daukarwa ‘yan Najeriya a lokacin yakin neman zabe na shekarar 2015.

A hirarsa da gidan Radio Trust, tsohon ministan ya ce a matsayinsa na wanda suka kafa jam’iyar APC ya zama wajibi ya fadi gaskiyar abin da ke faruwa.

“Babu wani lungu da sako na kasar nan ba mu shiga a lokacin yakin neman zabe ba musamman a Arewacin Najeriya, mun dauki alkawura amma babu alkawarin da muka iya cikawa.

“Idan aka waiwaya baya, za a lura cewa babu wani abu da muka tsinana a lokacin gwamnatinmu.”

Ya ce a lokacin yakin neman zabe, sun yi wa ‘yan Najeriya alkawarin samar da tsaro da farfado da tattalin arzikin kasar da kuma yakar cin hanci da rashawa, amma sai dai sun gaza cika duk alkawuran da suka dauka.

Dalung ya bayyana Buhari a matsayin mutum nagari kuma shugaba mai gaskiya, wanda kuma ta aminta da mutanen da ke tare da shi, duk da cewa su ne suka bata masa suna.

“Buhari mutumin kirki ne wanda ya aminta da duk makusantansa saboda tsammaninsa duk mutanen kirki ne, amma a yanzu a dalilinsu yana rayuwa cikin nadama.

“Saboda su ne suka kai shi suka baro suka bata masa suna, sannan suka hana gwamnatinsa rawar gaban hantsi,” in ji Dalung.

Tsohon ministan ya ce gwamnatin jam’iyar APC daga tsakanin shekarar 2015 zuwa 2019 ta samu nasarori, domin al’amuran tsaro a lokacin ba su tabarbare kamar yanzu ba.

Jaridar Aminiya

Tags: Muhammadu Buhari Solomon Dalung

Post navigation

Previous: Ƴan Sanda Sun Kama Kananan Yara Da Laifin Fashi Da Makami A Delta
Next: Zaftarewar kasa ta yi ajalin wasu mutane a Kamaru

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.