Skip to content
September 20, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Wike zai kulla alaka da Isra’ila don samar da tsaro a Abuja

October 10, 2023 2 minutes read

 

Hukumar Kula da Birnin Tarayyar Abuja a Nijeriya ta sanar da cewa za ta kulla alaka da kasar Isra’ila domin samar da tsaro da tallafa wa matasa da kuma samar da ayyukan yi.

Ministan Abuja Nyesom Wike ne ya bayyana haka a ranar Talata bayan ya karbi bakuncin jakadan Isra’ila a Nijeriya Mista Michael Freeman.

Ministan ya shaida wa jakadan na Isra’ila cewa Abuja na da yanayi mai kyau wanda za a iya noma kuma akwai shiri da gwamnati take da shi a kasa domin kafa manyan gonaki wadanda matasan Nijeriya za su samu ayyukan yi.

FCTA PRESS RELEASE

FCTA PARTNERS ISRAEL ON SECURITY, YOUTH EMPOWERMENT

The Federal Capital Territory Administration, FCTA will partner with the State of Israel to promote security, youth empowerment and job creation in the FCT. pic.twitter.com/aZ38uC2pBZ

— Official FCTA (@OfficialFCTA) October 10, 2023

A bangaren tsaro kuwa, Mista Wike ya bayyana cewa Abuja kamar sauran birane na duniya na fuskantar kalubale na tsaro inda ya ce kofa a bude take domin su hada hannu da Isra’ila don inganta tsaro a Abuja.

Wannan tattaunawar na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun karuwar rashin tsaro a Abuja musamman matsalolin garkuwa da mutane.

Ko a cikin watan nan na Satumba sai da aka sace mutum 19 a Karamar Hukumar Bwari da ke birnin tarayyar.

Haka kuma ‘yan sanda a Abuja sun sanar da kama masu garkuwa da mutane 11 a fadin birnin.

Tun bayan da Mista Wike ya samu mukamin Ministan Abuja, ya aiwatar da sauye-sauye da dama a birnin daga ciki har da sallamar shugabannin hukumomi 21 na birnin.

TRT Afrika

Tags: abuja Isra'ila Nyesom Wike

Post navigation

Previous: SON Bauchi Office Destroyed Substandard Products Worth Millions of Naira
Next: Sojojin Najeriya sun hallaka ƴan bindiga sama da 100

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.