Skip to content
September 14, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Sojoji sun kubutar da daliban Jami’ar Gusau wadanda aka sace jiya

October 15, 2023 1 minute read

Rundunar sojin Nijeriya ta bayyana cewa ta ceto dalibai hudu na Jami’ar Gusau wadanda aka sace a ranar Asabar 14 ga watan Oktoba da dare.

Rundunar ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook inda ta ce dakarunta na Operation Hadarin Daji da hadin gwiwar rundunar ‘yan sandan kasar ne suka yi aikin ceton.

Sojojin sun bayyana cewa an sace daliban ne a gidan da suke zaune wanda ke wajen jami’ar a Sabon Gida da ke yankin Damba a Gusau.

Sojojin sun bayyana cewa jim kadan bayan sace daliban suka samu kiran gaggawa wanda hakan ya sa suka toshe hanyoyin da barayin za su iya sulalewa.

A cewarsu, bayan an yi musayar wuta da barayin sai suka saki wadanda suka yi garkuwa da su suka gudu.

Satar daliban na zuwa ne makonni bayan an sace wasu gomman daliban na jami’ar wadanda har yanzu babu labarinsu.

Sai dai bayan an sace rukunin farko na daliban Jami’ar ta Gusau sojojin sun ce sun yi kokarin ceto shida daga cikinsu.

TRT Afrika Hausa

Tags: 'Yan Bindiga Gusau Sojojin Najeriya

Post navigation

Previous: WCS Trains Security Rangers To Protect Wildlife In Yankari 
Next: Jam’ian Tsaro Sun Garƙame Sakatariyar PDP Na Jihar Ondo 

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.