Skip to content
September 20, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Dalibin Jami’ar Gombe Ya Rasu Yana Tsaka Da Rubuta Jarrabawar Karshe

October 18, 2023 1 minute read

 

Wani dalibin Jami’ar Jihar Gombe da ke zangon karatu na karshe mai suna Abubakar Muhammad, ya rasu yayin da yake tsaka da rubuta jarrabawar kammala makarantar.

Dalibin dai na karatu ne a sashen koyon aikin Akanta na jami’ar.

Wani abokin karatun marigayin ya bayyanawa wakilinmu cewa marigayin ya zo dakin rubuta jarrabawa a ranar sai rashin lafiya ta kama shi inda nan take aka garzaya da shi zuwa cibiyar lafiya ta jami’ar dan duba lafiyarsa.

Sai dai a cewar majiyar, jikin dalibin ya tsananta, amma kafin nan rai ya yi halinsa, inda aka wuce da shi dakin adana gawarwaki a asibiti.

“Ya rasu a cibiyar lafiya ta jami’ar sannan daga bisani mataimakin shugaban sashen tsaro na jami’ar ya jagoranci daukar gawar zuwa dakin adana gawarwaki na asibitin kwararru na Jihar Gombe tare da wasu abokansa da kuma wasu jami’an jami’ar,” in ji dalibin.

Da wakilinmu ya tuntubi jami’in hulda da jama’a na jami’ar, Mohammed Abubakar, ya tabbatar da rasuwar dalibin.

Sai dai ya ce dama dalibin ba shi da lafiya a ranar tun kafin shigarsa dakin zana jarrabawar.

Jaridar Aminiya

Tags: Jami'ar Gombe Jarabawar

Post navigation

Previous: Ministan Tsaro Da Sakataren Gwamnatin Chadi Sun Ajiye Aikinsu kan Bidiyon Batsa
Next: ACReSAL organises Workshop on Gender Based Violence for stakeholders in Bauchi

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.