Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Bam Ya hallaka Mutane 20 A Yobe

November 1, 2023 1 minute read

 

Akalla mutane 20 ne suka mutu bayan da wani babur ya taka wani bam da ‘yan ta’addan Boko Haram suka dasa a jihar Yobe a yammacin ranar Talata.

Bam din ya tashi ne da misalin karfe 6:30 na yamma a kauyen Goni Mittiri da ke garin Gumsa a karamar hukumar Gaidam a jihar, kamar yadda shaidun gani da ido suka shaida wa LEADERSHIP.

An ruwaito an yi jana’izar kimanin mutane 17 da harin Boko Haram ya rutsa da su a safiyar ranar Litinin, yayin da suke dawowa daga makabarta, yayin da wani abu ya fashe.

Wasu majiyoyi sun ce an birne bam din ne a gefen hanya.

Daya daga cikin mazauna yankin ya ce, “Mun kidaya jimillar mutane 20 a wurin da lamarin ya faru, za mu yi jana’izar mutum 11 a wannan dare (ranar Talata).

“Sauran mutane tara da suka mutu za a birne su a gobe Laraba da karfe 9 na safe amma akwai ma’aurata – mata da miji wanda suke karbar magani a asibiti saboda raunukan da suka samu sakamakon fashewar bam din.”

Jaridar Leadership

Tags: Bam Boko Haram yan ta'adda Yobe

Post navigation

Previous: Wani Miji Ya Bukaci Matarsa Ta Biya Shi Miliyan 1.5 Kafin Ya Sake Ta
Next: Da Dumi-Dumi: Ƴan sanda Sun Kama Shugaban NLC A Imo

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.