Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Majalisar wakilai na binciken yadda aka kashe kuɗin tallafin Korona

November 3, 2023 2 minutes read

Majalisar wakilan Najeriya ta bai wa akanta-janar na ƙasar zuwa ranar juma’a, ya gabatar mata da cikaken bayanin yadda aka kashe sama da naira biliyan 100 na tallafin yaki da cutar korona, ko ya fuskanci fushinta.

Mataimakin shugaban kwamitin watsa labarai da wayar da kan jama’a na majalisar wakilan, Hon. Salisu Yusuf Majigiri ya shaidawa BBC cewa Majalisar ta yi iya bakin ƙoƙarin ta wajen samun waɗannan bayanai, sai dai ba ta samu haɗin kai daga ofishin akanta-janar ɗin ba.

Ya ce ‘‘akwai biliyoyin kuɗin waɗanda ake ganin sun salwanta a wannan tsakani, kuma amfanin kuɗin shi ne a tallafi rayuwar al’ummma da suka shiga wani hali a wannan tsakani na 2020 zuwa 2022’’

Ya yi bayanin cewa majalisar ta buƙaci bayanai daga akanta-janar ne saboda shi ne ke sane da lissafin duk wani abu da ya shafi dukiyar ƙasa, don haka ita majalisa shi ne tushen fara aikin ta don tantance ‘’mai ya shigo, mai ya fita, kuma da ya fita ina ya je’’

‘‘Kuɗi ne rukuni daban-daban, akwai wanda ake zargin wajen biliyan ɗari kuma akwai wasu daban. Wannan dai ƙadan ne daga cikin abubuwan da aka gabatarwa majalisa don bincike, kuma sakamakon binciken ne kaɗai zai tabbatar da gaskiyar lamarin’’

‘Akwai ayar tambaya kan kudaden tallafin korona a Najeriya’

Hon. Salisu ya ce kwamitin zai yi duk abin da ya dace don ganin an gudanar da sahihin bincike da nbazari game da yadda aka kashe kuɗin, sannan ya yi kira ga sauran hukumomin gwamnati su ƙara zage damtse don bai wa majalisar goyon baya a ƙoƙarin ta na tabbatar da gaskiya kan wannan batu.

Majalisar dai tana zargin cewa an karkatar da kuɗaɗen tallafin korona a ma’aikatu da hukumomin gwmanati, lamarin da ta ce ya ruruta matsalar da jama’ar Najeriya suka fuskanta a lokacin annobar.

A halin yanzu dai majalisar ta riga ta nemi a gabatar mata da dukkan bayanan da takardun shaidar yadda aka kashe kuɗin, a ranara Juma’a, kuma ta sha alwashin ɗaukar matakin ladabtarwa idan har wa’adin ya cika ba tare da an aikata umarnin nata ba.

Tags: Korona Majalisar Wakilai Tallafi

Post navigation

Previous: Matatar Mai Ta Dangote Za Ta Fara Aiki A Watan Disamba
Next: Albarka Radio obtained license to commence operation in Kaduna state

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.