Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Wata uwa ta cafke wanda ya yi garkuwa da ƴarta a wajan karbar kudin fansa a Zariya 

September 30, 2023 3 minutes read

 

Wata mahaifiya ta sami nasarar kama wanda ya yi garkuwa da ’yarta a wajan kai kudin fansa.

Sai dai bayan ta kama shi an gano cewa tuni ma har ya kashe ’yar tata kuma ya birne gawarta a gidansa da ke Karamar Hukumar Zariya a jihar Kaduna.

Binciken Aminiya ya gano wanda ake zargin mai suna Aminu Ibrahim mai shekaru 35 da haihuwa, ya yi garkuwa da Fatima Adamu mai shekara 23 da haihuwa, kuma ya kashe ta inda ya birne gawar a gidansa.

Wakilinmu ya ziyarci gidan da lamarin ya faru a layin Sadauki da ke gundumar Wusasa a Zariya, inda ya tattauna da mahaifiyar mamaciyar mai suna Nana Fatima.

Nana, wacce ta yi bayani cikin kuka ta ce, “Sati hudu da ’yata Fatima ta yi tafiya zuwa Kaduna suna, iuma tace ba za ta wuce kwana hudu ba.

“To bayan tafiyarta sai muka dinga kiran wayarta ba ta shiga, sai daga baya wani ya dauka ya ce wai Fatima tana wajensu kuma sai an ba shi Naira miliyan 3 kafin su sake ta.

“Daga nan ne muka gane cewa Fatima dai an yi garkuwa da ita ne.”

Nana Fatima ta kara da cewa to bayan sun fahimci haka sai suka kai rahoto ofishin ’yan sanda da ke Dan Magaji a Zariya.

Ta ce, “Bayan haka muka fara ciniki da wadanda suka kama ta har dai suka ce a kawo musu abin da ke hannunmu, inda na nemo Naira dubu dari da ke hannuna sannan muka yi mahada na kai musu kudin,” in ji Nana.

Sakamakon neman karin kudi da suka yi, Nana Fatima ta ce sai ta sa wani filinta a kasuwa domin sayarwa don ta haɗa kudin amma sai ba a sami mai saye ba har dai daga baya ta iya sake hada Naira dubu dari.

Ta ce daga nan sai ta kira mai garkuwa da mutanen inda ta sanar da shi cewa ta sake hada wasu kudin, kuma ya umurce ta da ta kai masa.

Ta ce, “To a wannan karon sai muka tafi da kanwa ta Hajara domin mu kai kudin, to muna tafiya muna waya da shi har ya ce mu zo kofar asibitin Wusasa, da ke Zariya can kuma sai ya ce mu dawo baya haka muka yi ta yi har muka hadu da shi tun da dama ni na san shi.

“Bayan haduwar mu sai yayi kokarin ya kwance kudin a hannuna amma na ki yarda tun da cikin mutane ne, to dama ya riga ya sauka daga kan babur din da ya kawo shi.

“Ana cikin haka sai na kwada ihu jama’a barawo don Allah a taimake ni. Nan da nan kuwa jama’a suka yi ca aka kama shi.

“Daga nanne aka kai shi ofishin ’yan sanda, inda ya yi bayanin yadda ya kashe ’ya ta Fatima sannan suka birne ta suka dora buhunan gawayi a inda suka rufe ta,” inji ta.

Jami’in hulda da Jama’a na Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ASP Mansir Hassan ya tabbatar da kama wanda ake zargin, sannan ya ce ya kuma kai jami’an ’yan sanda inda ta birne gawar.

Jaridar Aminiya

Tags: Garkuwa Kaduna Kudin Fansa Zaria

Post navigation

Previous: Wani ɗan Bindiga Ya Ƙaƙaba Wa  Manoma Haraji A Ƙauyukan Katsina
Next: Mutum 40 sun ɓata bayan kifewar Kwalekwale a Kebbi

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.