Home Security Yan Sanda Sun Kama Masu Satar Shanu, Sun kuma Kwato Shanu guda...

Yan Sanda Sun Kama Masu Satar Shanu, Sun kuma Kwato Shanu guda 10 a Bauchi

Daga Zainab Kasim Ibrahim

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta kama wasu da ake zargi da satar shanu guda biyu inda ta gano shanu 10 da aka sace a kauyen Maikwangi,na karamar hukumar Ningi.

Wadanda aka kama sun hada da Umar Usman, mai shekaru 24, da kuma Auwal Mohammed, mai shekaru 22, daga karamar hukumar Sabo, a Jihar Kaduna. An kama su ne a ranar 14 ga watan Agusta, 2025, bayan samun bayanan sirri.

Bisa ga sanarwar rundunar, jami’an ‘yan sanda daga ofishin‘yan sanda na Ningi tare da hadin gwiwar jami’an tsaro na wasu hukumomi, karkashin jagorancin DPO na Ningi, sun gudanar da samame har suka samu nasarar kama mutanen biyu.

A yayin da ake tuhumarsu, wadanda ake zargin sun amsa laifinsu inda suka bayyana cewa sun sace shanun ne daga wani makiyayi da ke dajin Gwamnare, a kauyen Maikwangi, kimanin wata daya da ya wuce.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya tabbatar da kama mutanen, inda ya nemi al’ummar Gwamnare da daukacin jama’a da su yada wannan bayani domin a gano ainihin masu shanun da aka sace.

Ya kara da cewa bincike na ci gaba, kuma daga bisani za a gurfanar da su a kotu.


Discover more from Albarka Radio

Subscribe to get the latest posts sent to your email.