Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

DSS Sun Kama Babban Editan jaridar Al-Mizan

September 27, 2023 2 minutes read

 

Jami’an Hukumar Tsaro ta DSS sun cafke Babban Editan jaridar Al-Mizan ta mabiya Shi’a, Ibrahim Musa, a Kano.

An kama shi ne a filin jiragen sama na Malam Aminu Kano da ke Kano a ranar Laraba, a kan hanyarsa ta tafiya kasar Saudiyya domin ibadar Umarah.

Jaridar Al-Mizan dai na fita ne kowanne mako a cikin harshen Hausa.

A cikin wata sanarwa da wani dan uwan mawallafin mai suna Abdullahi Usman ya fitar a ranar Laraba, ya tabbatar da kamun sannan ya bukaci a gaggauta sakin Ibrahim din.

Sanarwar ta ce, “Jami’an hukumar ba su bayar da kowanne irin dalili na kama shi ba, duk da sun san matsayinshi kan bukatar neman a saki Sheikh Ibrahim Zakzaky, wanda gwamnati ta kama a Zariyan Jihar Kaduna a shekara ta 2015.

“An kama Ibrahim Musa ne, wand yake tare da wata ’yar uwarsa mai suna Binta Sulaiman, lokacin da DSS ta kama shi a filin na Kano da sanyin safiyar Laraba, a kan hanyarsa ta tafiya Umarah.”

Sai dai Abdullahi ya ce Ibrahim ya yi kaurin suna wajen sukar lamirin kisan da kuma nuna wariyar da ake yi wa mabiya Shi’a da suka ce gwamnatin tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ta yi.

Sun kuma bukaci a gaggauta sakin shi ba tare da bata lokaci ba.

Jaridar Aminiya

Tags: DSS jaridar Al-Mizan

Post navigation

Previous: Gwamnatin tarayya ta musanta zargin sasantawa da ƴan bindiga a Zamfara
Next: Wike ya kori shugabannin hukumomi 21 na Abuja

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.