Skip to content
September 14, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Wike ya kori shugabannin hukumomi 21 na Abuja

September 28, 2023 2 minutes read

 

Ministan Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, Nyesom Wike, ya sallami shugabannin manyan hukumomi da ma’aikatun Abuja ashirin da daya.

Ministan ya bayyana haka ne a wata sanarwa da Anthony Ogunleye, mai magana da yawun ofishin ministan, ya fitar ranar Alhamis.

Sanarwar ba ta fadi dalilan da suka sa ministan ya kori shugabannin ma’aikatun ba. Sai dai tun da aka nada shi a mukamin minista, Mr Wike ya sha alwashin yin garambawul ga ma’aikatun birnin.

Ta kara da cewa an umarci mutanen su mika ragamar ofisoshinsu ga daraktoci mafi girman mukamai na ma’aikatunsu, tana mai cewa nan ba da jimawa za a maye gurbinsu.

Kazalika ya ce zai kawo gagarumin sauyi a birni na Abuja, wanda ya ce ana keta doka a fannoni daban-daban. Hasalima tuni Mr Wike ya soma rusa wasu gine-gine a birnin na Tarayyar Nijeriya, wadanda ya ce an yi su ba bisa ka’ida ba.

Ga jerin ma’aikatun da ministan na Abuja ya kora daga aiki:

Kamfanin Zuba Jari na Abuja

Hukumar Kula da Kasuwannin Abuja

Hukumar Sufuri ta Abuja

Hukumar Samar da Ci-gaban Gidaje da Gine-Gine ta Abuja

Kamfanin Ci-gaban Fasaha na Abuja

Ma’aikatar Fina-finai ta kasa da kasa da ke Abuja

Kamfanin Powernoth AICL Equipment Leasing Ltd

Hukumar Watsa Labarai ta Abuja

Hukumar Abuja Enterprise Agency

Hukumar Samar da Ruwa ta Abuja wato FCT Water Board

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Abuja

Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Abuja

Hukumar Kula da Asibitoci ta Abuja

Hukumar Kula da Muhalli ta Abuja

Hukumar Bayar da Tallafin Karatu ta Abuja

Hukumar kula da Kiristoci Masu zuwa Ziyara wurare masu Tsari

Hukumar Aikin Hajji ta Aabuja

Cibiyar Abuja Infrastructure Investment

Hukumar Inshorar Lafiya ta Abuja

Ma’aikatar da ke Kula da Garuruwan da ke Kewayen Abuja

Majalisar Kula da Cikin Birnin Abuja

TRT Afrika

Tags: abuja Nyesom Wike

Post navigation

Previous: DSS Sun Kama Babban Editan jaridar Al-Mizan
Next: Google Zai Raba ₦75m Ga ‘Yan Kasuwa 15 Masu Rabo

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.