Skip to content
September 20, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Wike Ya Yi Wankin Babban Bargo Wa EU Kan Zaben 2023

October 13, 2023 2 minutes read

 

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike ya yi wa Kungiyar Tarayyar Turai (EU) wankin babban bargo kan rahoton zaben shugaban kasa na 2023.

Ya ce rahoton bai bayar da hakikanin gaskiyar zaben da aka gudanar a kasar ba, amma ya haifar da mummunar fahimta a zukatan al’umma musamman a Jihar Ribas.

Wike ya nuna rashin jin dadinsa ne a lokacin da jakadan EU a NIjeriya, Samuela Isopi, ya kai masa ziyarar aiki a ofishinsa.

Ministan ya ce ya kamata Kungiyar EU ta kasance mai sa ido a zaben da ya gabata ba wai ta gabatar da wani rahoto da ba zai bayar da hakikanin tsarin dimokuradiyya a Nijeriya ba.

Tawagar masu sa ido a zaben na Kungiyar Tarayyar Turai (EUOM) ta bakin babban jami’inta, Barry Andres, a watan Yuni sun gabatar da rahotonsu na zaben Nijeriya da ya gabata, tare da bayyana wasu muhimman abubuwa guda shida da suka ba da shawarwari a kai.

Wike, ya ce dokokin Nijeriya ba za su iya zama daidai da na EU ba saboda suna da yanayi daban-daban.

Ya ce: “Ban yarda da Tarayyar Turai kan rahoton zaben Nijeriya ba. Ya kamata su kasance masu saka ido ne. Dokokin Nijeriya ba za su iya zama daidai da dokokin EU ba saboda suna da yanayi mabambanta.

“A Jihar Ribas, rahoton EU ya bambanta da abin da ya faru a can. Ta yaya za a iya kwatanta mutanen da suka yi imani da dimokuradiyya kuma suke aiki da ita a matsayin mutanen da ba su fahimci dimokuradiyya ba?

“Damuwarmu ita ce yadda za mu inganta tattalin arzikin kasa, dole ne mu hada kai tare da cimma matsaya kan fannonin ci gaba a Babban Birnin Tarayya da ma kasar baki daya.”

Da take mayar da martani, jakadiyar Tarayyar Turai a Nijeriya, Samuela Isopi, ta ce masu sa ido masu zaman kansu ne suka hada rahoton kuma ba shi da alaka da ayyukanta.

Ta yi alkawarin yin aiki tare da ministan don bunkasa ci gaba a yankin Abuja da ma kasar gaba daya.

Jaridar Leadership

Tags: EU Nyesom Wike Zaɓen 2023

Post navigation

Previous: Mutum 1,715 ƴan bindiga suka kashe cikin wata uku a Najeriya, cewar wani Rahoto
Next: An kama wasu mutum uku kan Sace Tirela Mai Dauke Da Kayan Miliyan 550

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.