Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Wani Miji Ya Bukaci Matarsa Ta Biya Shi Miliyan 1.5 Kafin Ya Sake Ta

October 31, 2023 2 minutes read

 

Wani dan kasuwa, mai suna Nura Ashiru, ya bukaci matarsa Zainab Bello wadda ta nemi da ya sake ta da ta biya shi Naira miliyan 1.5 a wata kotun shari’a da ke zamanta a Magajin Gari, a Jihar Kaduna.

Ashiru ya gabatar da bukatarsa ne bayan da matarsa ta bukaci kotu ta datse igiyar aurensu ta hanyar Khul’i, wato hanyar da mace ke mayar da sadakin da ta karba domin ta fanshi kanta daga auren.

“Matata ta yi min babbar asara. Ta lalata wayata ta kwashe wasu kayana, lamarin da ya sanya ni cikin bacin rai,” in ji shi.

Ya kuma roki kotun da kada ta bai wa matarsa rikon dansu ko da ta raba auren.

Tun da farko dai mai shigar da kara ta shaida wa kotun cewa a shirye ta ke ta mayar da kudin sadakin Naira 80,000 da ta karba daga hannun wanda ta ke kara sannan ta roki da kotun ta ba damar rikon yaronsu dan shekara uku a duniya.

Sai dai wadda ta shigar da karar ta musanta lalata wayar mijinta.

Alkalin kotun, Malam Isiyaku Abdulrahma, ya dage sauraren karar zuwa ranar 8 ga watan Nuwamba domin wanda ake kara ya gabatar da shaidunsa.

Jaridar Aminiya

Tags: Kaduna saki

Post navigation

Previous: Ƴan Fashin Daji Sun Sace Kawayen Amarya A Katsina
Next: Bam Ya hallaka Mutane 20 A Yobe

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.