Skip to content
September 14, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026 2 minutes read

By Melody Agwom Dauda

Sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya fitar da sakon taɓa zuciya domin murnar fara watan Ramadan na Shekarar 2026 a inda ya yi kira ga duniya baki ɗaya da ta rungumi ruhin zaman lafiya, tausayi da haɗin kai da wannan wata mai tsarki ke ɗauke da shi.

A cikin sakon nasa, Guterres ya jaddada cewa Ramadan ba lokaci ne na ibada da tunani kawai ba, wata ce ta ƙarfafa bege da zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Ya yi kira ga kowa da kowa da ya yi amfani da wannan lokaci wajen ƙarfafa haɗin kai da kuma nuna kulawa ga masu fama da rashin zaman lafiya a kasashe daban-daban na duniya.

“Ga Musulmai a duk faɗin duniya, watan Ramadan mai tsarki lokaci ne na tunani da addu’a.

“Ramadan kuma yana wakiltar zaman lafiya.”

Mista Antonio ya yi nuni da rikice-rikicen da ke ci gaba da addabar al’umma a kasashe daban-daban na duniya. Ya bayyana cewa an Afghanistan, Yemen, Gaza, Sudan da kuma wasu wurare, miliyoyin mutane na fuskantar “munanan tasirin rikici, yunwa, ƙaura, wariya da sauran matsaloli.”

“A cikin waɗannan lokuta masu wahala, mu saurari saƙon da Ramadan ke ɗauke da shi wanda ba ya gushewa.

“Don haɗa kan al’umma. Don kawo taimako da bege ga waɗanda ke cikin wahala. Kuma don kare haƙƙoƙi da mutuncin kowane mutum.”

Mista Antonio ya kara da cewa, “Kowace shekara, ina yin ziyara ta musamman zuwa al’ummar Musulmi masu azumi kuma ina buda baki da su. Kuma kowace shekara nakan dawo da kwarin gwiwa daga ruhin Ramadan na zaman lafiya da tausayi.

“Allah ya sa wannan wata Mai Tsarki ya zame mana abin da zai ƙarfafa mu mu yi aiki tare a matsayin ɗaya, domin gina duniya mai cike da zaman lafiya, karamci da adalci ga kowa da kowa.

“Ramadan Kareem”.

Post navigation

Previous: Sa’adu Zungur University orients new Social Science students on campus life, drug abuse, career development
Next: ASR Africa Commissions Modern Hospital in Bauchi, Hands Over Facility to Nigeria Customs Service

Related Stories

  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025
  • Labarai

Matasa da ‘Yan Majalisa Sun Tattauna a Bauchi Don Kara Karfafa Dimokuradiyyar Shigo da Jama’a

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.