Skip to content
September 17, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

An kama malamin sakandare kan zargin fyade a Ogun 

November 8, 2023 2 minutes read

 

An kama wani malamin makarantar sakandare a Jihar Ogun bisa zargin yi wa wata budurwa fyade.

Olaniran da ake zargin, malamin lissafi ne a makarantar Ebenezer Grammar School da me Iberekodo, Abeokuta Jihar Ogun.

Kwamishinar harkokin mata ta jihar, Adijat Olaleye ce ta bayyana cewa an kama malamin ne a ranar Asabar, a lokacin da wata daga cikin mukarrabanta ta samu kira cewar wani malamin ya yi mata fyade.

Kwamishiniyar ta ce ma’aikatar ta je inda lamarin ya faru inda aka yi gwaje-gwaje tare da mika rahoton ga ’yan sanda.

“Daga baya mun tafi tare da ’yan sanda zuwa gidan wanda ake zargi, amma da aka kwankwasa ya ki bude kofar. Mun samu dan uwansa wanda shi ne ya taimaka mana muka shiga gidan,” in ji ta.

Adeleye ta bayyana cewa da suka shiga harabar gidan wanda ake zargin, “mun ji kukan yarinya tana neman agaji, kuma ’yan sanda sun taimaka mun kama Mista Olaniran Lateef Adewale, wani malamin lissafi na makarantar sakandare ta Ebenezer Grammar School Iberekodo, Abeokuta. ”

Kwamishinar ta kara da cewa yarinyar tana kuka a dakin malamin a lokacin da aka kama shi ta kuma zarge shi da yin lalata da ita da kuma yin barazanar kashe ta.

An tsare wanda ake zargin a hedikwatar ’yan sandan jihar Ogun domin ci gaba da bincike.

Jaridar Aminiya

Tags: Fyade Ogun

Post navigation

Previous: An daure wani manomi shakara 6 kan noma tabar wiwi
Next: Anyi wa Fasto dukan kawo wuƙa kan satar Mazakuta

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.