Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

An daure wani manomi shakara 6 kan noma tabar wiwi

November 8, 2023 2 minutes read

 

Babbar kotun tarayya da ke Ibadan ta yanke wa wani manomi hukuncin daurin shekara shida kan laifin noma da kuma ta’ammali da tabar wiwi.

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), ce ta gurfanar da manonmin bisa tuhume-tuhume biyu da suka hada da noma da kuma ta’amalli da miyagun kwayoyin.

  • Manoma 4 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Nasarawa
  • Kotu ta ayyana Minista a matsayin Sanatan Filato bayan soke zabe

Mai shari’a A. Okeke ce ta yanke masa huukuncin daurin shekara 6 ne bayan lauya mai shigar da kara, Misis Anne Balogun ta gabatar da shi.

Okeke ta yanke masa hukuncin daurin shekara uku kan laifin noma rabin hekta na tabar wiwi a kauyen Ibu-Ade da ke Apata a Ibadan.

Ta kuma sake daure shi na shekara uku kan laifin safarar kilogiram 64 na tabar, kamar yadda Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito.

Alkalin ta ce “Na yanke masa hukuncin daurin shekara uku a kan laifi na daya da kuma daurin shekara uku a kan laifi na biyu. Hukuncin zai fara aiki a lokaci guda daga ranar da aka kama,” in ji ta.

NAN ta ruwaito cewa alkalin ta kuma umarci NDLEA da ta lalata abubuwan da aka kama idan ba a daukaka kara a cikin kwanaki 30 ba.

Tun da farko dai lauyan mai shigar da kara ya shaida wa kotun cewa an kama wanda ake tuhumar ne a ranar 12 ga watan Satumba a kauyen Ibu-Ade bisa zargin yin noma da kuma yin mu’amala da tabar wiwi.

Ta kira jami’in NDLEA, Olaniyan Olutayo a matsayin shaida, wanda ya kawo tabar wiwi mai nauyin kilo 64 a matsayin hujja.

Lauyan wanda ake kara, Mista Adetola Babalola, ya roki da a yi masa sassauci wajen yanke masa hukunci.

Jaridar Aminiya

Tags: Kotu Tabar Wiwi

Post navigation

Previous: Islamic scholars urged to shun unguarded utterances
Next: An kama malamin sakandare kan zargin fyade a Ogun 

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.