Home News Uwargidan Gwamnan Jihar Bauchi Ta Kaddamar Da Rabon Maganin Azithromycin Don Rage...

Uwargidan Gwamnan Jihar Bauchi Ta Kaddamar Da Rabon Maganin Azithromycin Don Rage Yawan Mutuwar Yara ‘Yan Ƙasa da Shekara Biyar

Daga Zainab Faruq

Uwargidan Gwamnan Jihar Bauchi, Hajiya Aisha Bala Abdulkadir Mohammed, ta kaddamar da rabon maganin Azithromycin ga yara ‘yan shekaru 1 zuwa 59 wata, a wani mataki na rage yawan mace-macen yara ƙanana a fadin jihar.

An gudanar da bikin ƙaddamarwar a garin Bauchi ranar Litinin, wanda ya nuna fara aiwatar da aikin ƙarƙashin shirin SARMAAN II. Aikin na gudana ne ƙarƙashin hadin gwiwar Hukumar Bunƙasa Lafiyar Firamare ta Jihar Bauchi (BSPHCDA), tare da Mitosath da sauran abokan hulɗa na ci gaba.

A jawabin ta yayin bikin, Hajiya Aisha ta bayyana wannan shiri a matsayin muhimmin mataki wajen yakar cututtukan yara kamar su cutar numfashi, gudawa, trachoma da sauran cututtuka da ke addabar yara ƙanana. Ta bayyana cewa gwamnatin jihar Bauchi na da ƙwarin guiwa wajen ba da fifiko ga lafiyar mata da yara, inda ta jaddada cewa gwamnatin ta riga ta biya kuɗaɗen da ake buƙata don aiwatar da muhimman shirye-shiryen lafiya kamar ciyar da yara, shirin tsara iyali da kuma ayyukan lafiyar firamare.

“Ina da kwarin guiwar tallafa wa irin waɗannan shirye-shiryen da ke canza rayuwa, musamman ma domin inganta lafiyar mata da yara,” in ji Hajiya Aisha, wadda ita ce shugabar gidauniyar Almuhibba Foundation. Ta kuma bayyana cewa gidauniyar ta bayar da guraben karatu 50 ga ‘yan mata da ke karantar Ilimin Nas da sauran fannoni a Jami’ar Almuhibba, a kokarin ƙarfafa bangaren lafiyar jihar.

Uwargidan Gwamnan ta yabawa Mitosath, Cibiyar Binciken Lafiya ta Ƙasa (NIMR), Solina, eHealth Africa da Gates Foundation bisa goyon bayan da suke bayarwa wajen bunƙasa tsarin kiwon lafiya a jihar. Ta kuma yi kira ga shugabannin kananan hukumomi da matansu, sarakuna da malaman addini da su taimaka wajen wayar da kan iyaye da masu kula da yara domin tabbatar da cewa duk yara masu cancanta sun amfana da maganin.

Ta tabbatar wa al’umma cewa maganin Azithromycin lafiyayye ne kuma yana da tasiri, inda ta roƙi jama’a da su ba da haɗin kai ga ƙungiyoyin da za su rika yawo gida-gida domin rabon maganin.

A nasa jawabin, Kwamishinan Lafiya da Jin Daɗin Jama’a na jihar, Dr. Sani Muhammad Dambam, ya bayyana cewa Azithromycin na da amfani wajen kare yara daga cututtuka da dama da kan kashe su da wuri, ciki har da cutar huhu, gudawa da trachoma. Ya kuma tabbatar da cewa ma’aikatar lafiyar jihar za ta ci gaba da haɗin gwiwa da kungiyoyin tallafi domin samar da ingantattun ayyukan lafiya a fadin jihar.

Haka zalika, Shugaban Hukumar Lafiya ta Firamare ta Jihar Bauchi, Dr. Rilwanu Mohammed, ya bayyana cewa rabon maganin zai gudana ta hanyar yawo gida-gida, kuma zai ɗauki tsawon kwanaki biyar. Ya bayyana fatansa cewa wannan mataki zai taimaka matuƙa wajen rage mace-macen yara a jihar.

Wakilan Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya, Hukumar Raya Lafiyar Firamare ta Ƙasa, Gates Foundation da Mitosath sun gabatar da saƙonnin ban girma inda suka jaddada aniyar su na ci gaba da tallafa wa jihar Bauchi wajen inganta harkar kiwon lafiya.

Rabon maganin Azithromycin yana ɗaya daga cikin matakan da ke da nufin rage yawan mace-macen yara da inganta lafiyar al’umma, musamman a yankunan da ke da buƙatar kulawar lafiya ta musamman.


Discover more from Albarka Radio

Subscribe to get the latest posts sent to your email.