Skip to content
September 20, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Ministan Tsaro Da Sakataren Gwamnatin Chadi Sun Ajiye Aikinsu kan Bidiyon Batsa

October 18, 2023 1 minute read

Ministan Tsaron Chadi, Daoud Ibrahim da Sakataren Gwamnatin Kasar, Haliki Choua Mahamat, sun ajiye ayyukansu bayan fitar wasu bidiyoyinsu na batsala guda biyu.

Rahotanni sun ce jami’an gwamnatin sun ajiye aikin nasu ne a ranar Laraba, bayan bidiyoyin nasu sun karade gari musamman a kafafen sada zumunta na zamani.

Kakakin Firaministan kasar, Saleh Kebzabo ne ya ce gwamnatin ta amince da ajiye aikin nasu, kodayake sanarwar ba ta yi cikakken bayani ba.

Bidiyoyin dai da aka yada a ranakun Lahadi da Litinin, sun nuna mukarraban gwamnatin suna mu’amala da wasu.

Sai dai kamfanin dillancin labarai na Reuters bai iya tabbatar da sahihancin bidiyoyin ko jin ta bakin tsofaffin jami’an gwamnatin domin su mayar da martani a kai ba.

Ba kasafai dai ake samun badakalar fitar bidiyoyin batsa ba a Chadi, wacce galibin ’yan kasar Musulmai ne.

NAN/Jaridar Aminiya

Tags: Bidiyon Batsa Chadi Ministan Tsaro Sakataren Gwamnati

Post navigation

Previous: Ƴan bindiga sun kashe mutane da dama, sunyi garkuwa da wasu a Kano
Next: Dalibin Jami’ar Gombe Ya Rasu Yana Tsaka Da Rubuta Jarrabawar Karshe

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.