Home Labarai Sojoji sun kashe ƴan Boko Haram 6 a Yobe

Sojoji sun kashe ƴan Boko Haram 6 a Yobe

 

Sojojin bataliya ta 159 da ke a garin Geidam a sashe na biyu na rundunar sojin hadaka ta Operation Hadin Kai, sun yi wa ‘yan ta’adda kwanton bauna, wanda hakan ya ba su nasarar kashe ‘yan ta’adda shida. 

A cikin sanarwar da mataimakin mukaddashin darakatan hulda da jama’a na rundunar, Kaftin Muhammad Shehu ya fitar a ranar Alhamis ta ce, sojojin sun kuma kwato bindigun AK-47 biyu, babura biyu da kuma wayar hannu a lokacin fafatawar.

Sanarwar ta ce, sojojin sun yi nasarar ne a aikin da suka yi a ranar 25 na watan Okutubar 2023 a Kauyen Jororo na karamar hukumar Geidam a jihar Yobe.

Kazalika sanarwar ta kara da cewa, wasu daga cikin ‘yan ta’addar sun tsere yayin fafatarwar dauke da harbin albarusai a jinkinsu.

Bugu da kari, sanarwar ta ce, a wani aikin da sojin suka gudanar a ranar Alhamis a kauyukan Bajingo da Kurnawa a yankin Babbangida a karamar hukumar Tarmuwa a Yobe, sojin bataliya ta 233, sun kashe ‘yan ta’adda hudu sun kwato makamai da babura da sauransu.

Jaridar Leadership

Discover more from Albarka Radio

Subscribe to get the latest posts sent to your email.