Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Ƴan Boko Haram sun kai hari wa tawagar gwamnan Yobe

November 18, 2023 2 minutes read

 

Akalla jami’an tsaron gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni shida ne suka samu rauni yayin wani harin da ‘yan ta’addar Boko Haram suka kai musu a hanyar Maiduguri zuwa Damaturu.

Gwamna Buni yana Maiduguri tare da manyan baki domin halartar taro karo na 24 a Jami’ar Maiduguri (UNIMAID) lokacin da lamarin ya faru.

Gwamnan da ‘yan tawagarsa wadanda suka samu rakiyar gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, sun tafi Abuja a jirgin sama ta sansanin sojin sama da ke Maiduguri.

Majiyoyin leken asiri sun bayyana wa Zagazola Makama, wani kwararre kan yaki da tada kayar baya kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, cewa motocin jami’an tsaron da ke cikin ayarin gwamnan, ‘yan ta’addar sun farmake su a babbar hanyar Jakana.

Majiyar ta ce ‘yan ta’addar sun harbe sojojin da ke jagorantar ayarin motocin MRAP da wata motar bindigu da kuma wata motar da ke jigilar ‘yan sanda da jami’an DSS.

“Sai dai sojojin sun mayar da martani ta hanyar bude wuta, lamarin da ya tilasta wa ‘yan ta’addar tserewa, abin takaici, sojoji biyu da suka hada da direba daya da ‘yansanda hudu sun samu raunuka.

“Jami’an tsaro sun dawo Yobe lafiya, yayin da aka kai wadanda suka jikkata asibiti domin kula da lafiyarsu,” in ji Makama.

Jaridar Leadership

Tags: Boko Haram DSS Gwamna Mai Maka Buni Sojoji Yobe

Post navigation

Previous: Sojojin sunyi kutse ofishin EFCC domin kwato ƴan uwansu
Next: Bauchi state government to deal with Salary and payroll saboteurs.

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.