Akalla jamiâan tsaron gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni shida ne suka samu rauni yayin wani harin da âyan taâaddar Boko Haram suka kai musu a hanyar Maiduguri zuwa Damaturu.
Gwamna Buni yana Maiduguri tare da manyan baki domin halartar taro karo na 24 a Jamiâar Maiduguri (UNIMAID) lokacin da lamarin ya faru.
Gwamnan da âyan tawagarsa wadanda suka samu rakiyar gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, sun tafi Abuja a jirgin sama ta sansanin sojin sama da ke Maiduguri.
Majiyoyin leken asiri sun bayyana wa Zagazola Makama, wani kwararre kan yaki da tada kayar baya kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, cewa motocin jamiâan tsaron da ke cikin ayarin gwamnan, âyan taâaddar sun farmake su a babbar hanyar Jakana.
Majiyar ta ce âyan taâaddar sun harbe sojojin da ke jagorantar ayarin motocin MRAP da wata motar bindigu da kuma wata motar da ke jigilar âyan sanda da jamiâan DSS.
âSai dai sojojin sun mayar da martani ta hanyar bude wuta, lamarin da ya tilasta wa âyan taâaddar tserewa, abin takaici, sojoji biyu da suka hada da direba daya da âyansanda hudu sun samu raunuka.
âJamiâan tsaro sun dawo Yobe lafiya, yayin da aka kai wadanda suka jikkata asibiti domin kula da lafiyarsu,â in ji Makama.
Jaridar Leadership
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.









