Home News Gidauniyar Wunti Al-khair Ta Yi Gargadi Kan Masu Amfani Da Sunanta Ba...

Gidauniyar Wunti Al-khair Ta Yi Gargadi Kan Masu Amfani Da Sunanta Ba Bisa Ka’ida Ba

Daga Mubarak Aliyu Kobi

Gidauniyar Wunti Al-khair Foundation ta nesanta kanta daga kungiyoyi da wasu daidaikun mutane da ke gudanar da ayyuka da sunanta ba tare da izini ba, tana mai bayyana irin wannan aiki a matsayin sojan gona.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Gidauniyar ta jaddada cewa dole ne a guji amfani da sunanta wajen gudanar da shirye-shirye, taruka ko bayar da tallafi, koda kuwa da kyakkyawar manufa, ba tare da samun izinin ta ba. Ta bayyana cewa wannan mataki zai taimaka wajen hana bata-gari amfani da sunan Gidauniyar wajen aikata ayyukan da ba su dace ba.

Gidauniyar ta kuma bayyana cewa ba ta da alaka da harkokin siyasa, tare da jan hankalin jama’a kan cewa ba ta amincewa da duk wani yunkuri na amfani da sunanta wajen shirya taron siyasa ko amfani da kafafen yada labarai wajen yada manufofin siyasa.

Ta kara da cewa kamar yadda aka saba, Gidauniyar Wunti Al-khair Foundation na gudanar da ayyukan jin kai da bayar da tallafi ga mabukata a cikin al’umma, ba tare da wata manufa ta daban ba, tare da kiyaye adalci ba tare da nuna banbancin addini, kabila ko jam’iyya ba.

Gidauniyar ta bayyana cewa wannan gargadi ya zama dole domin jan kunne, tare da sanar da cewa za ta dauki mataki kan duk wanda ya yi kunnen uwar shegu, inda ta ce za ta bai wa hukumomin tsaro damar yin aikinsu idan aka ci gaba da karya wannan umarni.

“Idan kunne yaki ji, jiki ya tsira,” in ji sanarwar.

– Hukumar Gudanarwa, Wunti Al-khair Foundation


Discover more from Albarka Radio

Subscribe to get the latest posts sent to your email.