Skip to content
September 20, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Shugaban karamar hukumar Lokoja ya rasu

November 10, 2023 1 minute read

 

Allah Ya yi wa Shugaban Karamar Hukumar Lokoja, Honarabul Muhammed Danasabe Muhammed rasuwa a Jihar Kogi.

Aminiya ta ruwaito cewa an tabbatar da rasuwarsa da misalin karfe 4:30 na Asubahin wannan Juma’ar a wani asibiti a Lokoja, babban birnin jihar.

Bayanai sun ce an garzaya da marigayin zuwa asibiti ne bayan ya yanke jiki ya fadi a gidansa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, Danasabe na daya daga cikin ’yan siyasar da ke sahun gaba-gaba wajen halartar taruka a shirye-shiryen zaben gwamnan jihar da za a yi a gobe Asabar.

Wata majiya daga bangaren iyalansa ta ce an mika Danasabe Asibitin Shifa da ke Lokoja bayan ya yanke jiki ya fadi a gidansa cikin dare kafin wayerwar gari Juma’a.

Majiyar ta ce za a yi jana’izarasa bayan sallar Juma’a sannan a binne gawarsa a makabartar Unguwar Kura.

Ya rasu ya bar mahaifiyarsa, mata da kuma ’ya’ya.

Kawo yanzu dai masu makoki da alhini sun yi ta tururuwa a gidan mamacin domin jajanta wa iyalansa.

Jaridar Aminiya

Tags: Kogi Lokoja

Post navigation

Previous: Weather forecast, not against Islamic teachings – Dr. Hamza Abubakar
Next: Standard Organization of Nigeria Warns Public Against Consumption of Expired Food Items.

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.