Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya naÉa tsohon Gwamnan Jigawa Muhammad Badaru ministan tsaron Æasar.
Kazalika, tsohon Gwamnan Zamfara Bello Matawalle ne zai taimaka masa a matsayin Æaramin ministan tsaro.
Tsohon Gwamnan jihar Ribas da ke kudancin Æasar, Nyesom Wike, shi ne ministan Abuja, yayin da Maryam Mairiga daga Kano za ta yi aiki a matsayin Æaramar ministar Abuja.
Wata sanarwa ce daga fadar shugaban Æasa ta bayyana sunayen ministocin da ma’aikatunsu a yammacin Laraba.
Mutum 45 majalisar dattawa ta tantance kuma ta tabbatar a matsayin ministocin na Tinubu, abin da ke nufin za a sanar da sauran nan gaba.
Ga jerin sunayen ministcoin da ma’aikatunsu:
Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin na Dijita – Bosun Tijani
Æaramin Ministan Muhalli – Ishak Salaco
Ministan KuÉi da Tattalin Arziki – Wale Edun
Ministar Harkokin Teku da Tattalin Arziki – Bunmi Tunji
Ministan Lantarki – Adedayo Adelabu
Æaramin Ministan Lafiya da Walwalar Al’umma – Tunji Alausa
Ministan Maâadanai – Dele Alake
Ministan Yawon BuÉe-Ido – Lola Ade-John
Ministan Sufuri – Adegboyega Oyetola
Ministan Kasuwanci da Zuba Jari – Doris Anite

Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.








