Skip to content
September 16, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Wata Mata ta yi kashin fasassun kwalabe a Kalaba

October 6, 2023 2 minutes read

 

A wani yanayi mai matukar daure kai, wata mata mai matsakaitan shekaru mai suna Nkechi Blessing Nwobodo, ta yi kashin wasu fasassun kwalabe a Kalaba, babban birnin jihar Kuros Riba.

Nkechi, kamar yadda wakilinmu ya samu labari na zaune ne a garin Ifo da ke jihar Ogun.

A cewar matar, a zantawarta da Aminiya ranar Juma’a, “Na biyo tawagar ’yan uwana mata a motar haya daga Igun zuwa Legas da kuma sauran wasu jihohin kasar nan za mu tafi ziyarar Ibada wani kauye da ake kira Biakpan yankin Karamar Hukumar Biase da ke jihar Kuros Riba.

“Akwai wani rafi mai ruwan mu’ujiz da ruwansa yake wucewa ta gefen wurin ibadar da muka je sauke farali na tsarin addinin mu na Kiristanci bangaren Olumba.”

Ta ci gaba da cewa, “Mun yi imani ruwan yana warkar da cutuka ko wanne irin mutum yake fama da shi da mu mabiya muka yi imani da hakan.

“Mu mabiya darikar Brotherhood wato ta Olumba Olumba Obu. Sai daukacinmu muka shiga cikin ruwan rafin muna yin kurme saboda mu samu waraka daga cututtukan da suke damun mu a jikinmu a wannan kauye.

“Dama kuma ina fama da yawan laulayi da ciwon jiki sai na yanke shawarar bari in debi ruwan ins ha in yi wanka da shi ko na samu lafiya.

“Bayan mun gama aikin ziyarar ibadar mun koma gida kwanaki kadan sai na rika jin ciwon mara da ciwon baya kafin mu baro Biakpan zuwa gida Kalaba.

“Tun Kafin ma mu gama abin da muke yi na ziyarar ibadar a Kalaba na mayar da ruwan nan da na debo.

“Daga Nan fa sai na fara jin wasu abubuwa na motsi a cikina kamar su fito, na ji na matsu, sai na yi wuf na tafi bandaki naj e na tsuguna. Ina tsugunen ne na rika jin motsin wasu abubuwa a dubura ta na sanya hannu in jawo su.

“Nan fa na tsorata saboda yadda na rika jawo abubuwan suna fadowa ne har suka gama fita ban damu ba sai na Sanya waya ta ta hannu na dauki hoton abin da na kasayar sai na ga ashe wasu balli-ballin fasassun kwalabe ne na kasayar,” in ji Nkechi.

Jaridar Aminiya

Tags: Kalaba Kwalabe

Post navigation

Previous: Bauchi State University Students Launched E-book
Next: Gwamnan Kano Ya Yi Hayar Lauyan Tinubu Ya Wakilci Shari’arsa A Kotu

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.