Skip to content
September 14, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Ƴan sanda sun kama wadanda ake zargi da sace daliban Jami’ar Jos

October 6, 2023 (Last updated: October 6, 2023) 2 minutes read

Ƴan sandan sun kama wadanda ake zargi da sace daliban Jami’ar Jos

An kama wasu ƴan bindiga da ake zargin su da hannu a sace ɗaliban Jami’ar Jos da ke arewa ta tsakiyar Nijeriya.

Ƴan bindigan biyu na cikin mutum 91 da aka kama kan aikata mugwayen laifuka daban-daban a yankin, a yayin da dakarun tsaro ke zafafa kai samame kan wasu ƙungiyoyin masu tayar da zaune tsaye.

An kama waɗanda ake zargi da sace mutanen ne bayan wani samame da aiki na musamman da aka ƙaddamar na tsawon wata guda, da suka yi sanadin da jami’an tsaro suka gano maɓoyarsu, kamar yadda mai magana da yawun wata rundunar soji ta musamman a Jihar Filato da ake kira Operation Safe Haven ya faɗa a wata sanarwa.

Satar mutane don neman kuɗin fansa

Sace-sacen mutane don karɓar kuɗaɗen fansa inda har ɗaliban jami’a ma ba su tsira ba, ya zama ruwan dare a Nijeriya.

An saki waɗanda aka sace daga Jami’ar Jos ɗin bayan da iyayensu suka bai wa ɓarayin wasu kuɗaɗe da ba a faɗi yawansu ba, kamar yadda kafafan yaɗa labaran ƙasar suka ce.

Satar mutane don karɓar kuɗin fansa da ƴan bindiga ke yi har yanzu wani babban ƙalubale ne ga jami’an tsaro a Nijeriya, inda a wasu lokutan har a kan kashe mutanen da aka sace ɗin.

Ƴan sandan Nijeriya na ba da shawarar cewa bayar da kuɗin fansa da ake yi ga masu satar mutanen kan rura wutar matsalar, inda suke gaya wa iyalan waɗanda aka sace cewa su daina biyan kudin fansar.

TRT Afrika

Tags: 'Yan Bindiga Jos

Post navigation

Previous: Mutane 563 sun rasa muhallinsu sanadiyyar ambaliyar ruwa a Adamawa
Next: Bauchi State University Students Launched E-book

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.