Home Politics Ƙungiya Ta Baƙaci INEC Ta Soke Abubakar Saddique Daga Yi Wa APC...

Ƙungiya Ta Baƙaci INEC Ta Soke Abubakar Saddique Daga Yi Wa APC Takara a Bauchi

Wata Æ™ungiya mai zaman kanta, mai suna Accountability and Democratic Project (ADEP) ta rubutawa shugaban Hukumar ZaÉ“e Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC da ya cire sunan tsohon babban hafsan sojojin sama na Æ™asa, Abubakar Saddique daga yi wa jam’iyar APC takara a jihar Bauchi.

Kungiyar ta nuna bukatar neman cire sunan Sadique a matsayin É—an takara na cikin wata takarda da rubuta ta kuma aike wa INEC.

Kungiyar ta yi koken cewa dan takarar bai gabatar da cikakkun takardunsa ga hukumar zaben, kamar yadda doka ta tanada ba.

A cewar kungiyar, Air Marshall Abubakar bai sanya wasu muhimman takardunsa waÉ—anda za su tabbatar da bayanan da ya cike a form din INEC mai suna EC 9 ba.

Abubakar Sadique a ya riƙe muƙamin babban hafsan sojan sama kafin ritayarsa da kuma shiga siyasa.

Ya zama É—an takarar jam’iyyar APC a Bauchin ne bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben fidda-gwani wanda aka gabatar a cikin watan Mayu.


Discover more from Albarka Radio

Subscribe to get the latest posts sent to your email.