Dakarun sojin Najeriya sun yi wa ‘yan ta’adda kwanton Éauna, inda suka kashe 39 daga cikinsu tare da kama 159 a jihohin Borno da Yobe.
Daraktan yaÉa labarai na shalkwatar tsaron Æasar Manjo Janar Edward Buba, ne ya bayyana haka ga manema labarai a lokacin wani taron manema labarai a shalkwatar tsaron Æasar da ke Abuja.
Manjo Janar Edward Buba, ya ce dakarun Æasar sun sha alwashin ci gaba da fatattakar mutanen da ke yi wa zaman lafiyar Æasar zagon Æasa.
Daraktan yaÉa labaran shalkwatar tsaron ya ce dakarun sojin saman Æasar sun Æaddamar da hare-hare ta sama kan gungun ‘yan ta’adda a dajin Sububu da ke Kankara a jihar Katsina, tare da wargaza sansanoninsu.
Ya Æara da cewa dakarun rundunar Hadin Kai da ke aiki a yankin arewa maso gabashin Æasar, sun kama manyan kwamandojin Æungiyar Boko Haram da na ISWAP a garuruwan Gwoza da Tarmuwa da ke jihohin Borno da Yobe.
Manjo Janar Buba ya ce farmakin da sojojin suka kai ya tilasta wa wasu ‘yan ta’addan ajiye makamansu tare da kuÉutar da wasu mutane da mayaÆan suka kama da Æwato makamai masu yawa.
BBC Hausa
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.








