Shugaban gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ya nada ministoci 21, karkashin jagorancin sabon Fira Ministan kasar.
Shugaban mulkin sojin, Janar Abdoulrahamane Tchiani ya sanar da mambabin majalisar ministocin ne a ranar da kungiyar ECOWAS za ta fara taron da za ta cim-ma matsaya kan sabon matakin da za ta dauka kan juyin mulkin Nijar din.
Tsohon madugun âyan tawaye ya kafa kungiyar neman mai da Bazoum kan mulkin Nijar
Fira Minista Ali Mahaman Lamine Zeine da sojojin suka nada ne zai jagoranci ministocin, wadanda daga cikinsu sojoji za su jagoranci maâaikatu shida â tsaro, harkokin cikin gida, lafiya, sufuri, muhalli da kuma matasa da wasanni .
Ga jerin sunayen ministocin:
Fira minista kuma Ministan KuÉi da Tattalin arziki â Lamine Zeine Ali Mahamane
Karamin Ministan Tsaron Æasa â Laftanar-Janar Salifou Mody
Karamin ministan harkokin cikin gida da tsaron alâumma â Birgediya-Janar Mohamed Toumba
Ministan Matasa da Wasanni â Kanar-Manjo Abdourahamane Amadou
Ministan Lafiya da Walwalar Jamaâa â Kanar-Manjo Garba Hakimi
Ministan sufuri â Kanar Salissou Mahaman Salissou
Ministan Muhalli da Tsafta â Kanar Maizama Abdoulaye
Ministar Ilimi da Koyar da Sanaâoin Hannu da BunÆasa Harsunan Æasa â Elizabeth Cherif
Ministar Kwadago da Samar da Ayyukan â Aissatou Abdoulaye Tondi
Ministan Jin Kai da Agajin Gaggawa â Aissa Lawan Wandarama.
Ministan Harkokin Waje da HaÉa kan âYan Nijar Mazauna Ketare â Bakary Yaou Sangare
Ministan Kula da Majalisar Æasa da Tabbatar da Lafiyar Cikin Gida â Soumana Boubacar
Ministan Noma da Kiwo â Mahaman Elhadj Ousmane
Ministan Ilimi Mai Zurfi da Binciken Kimiyya da Fasaha â Farfesa Mahamadou Saidou
Ministan Shariâa da Kare âYancin Dan-Adam â Alio Daouda
Ministan Tsare-tsaren da Samar da Gidaje â Salissou Sahirou Adamou
Ministan Man Fetur da Maâadinai da Makamashi â Mahaman Moustapha Barke
Ministan Yawon BuÉe Ido da Sanaâoi â Guichen Agaichata Atta
Ministan Sadarwa da BunÆasa Fasahar Zamani â Sidi Mohamed Raliou
Ministan Kasuwanci da Masanaâantu â Seydou Asman
Ministan Harkokin KuÉi a Ofishin Firaminista â Moumouni Boubacar Saidou
Hakan kuwa na zuwa ne washegarin da Janar Tchiani ya karbi bakuncin Khalifan Darikar Tijjaniyya na yakin Yammacin Afirka, Malam Muhammadu Sanusi II a birnin Yamai, bayan gwamnatin sojin ta ki amincewa da ziyarar wakilan ECOWAS da kasashen duniya domin sulhu.
A farkon makon nan ne sojojin suka nada tsohon ministan kudin kasar, Ali Mahaman Lamine Zeine a matsayin fira minista, kimanin mako uku bayan sun kifar da gwamnatin shugaba Mohamed Bazoum, da har yanzu suke tsare da shi.
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.








