Shugaba Bola Tinubu ya umarci ayarin malaman addinin Musulunci da ke shiga tsakani a rikicin Jamhuriyar Nijar su koma wajen shugabannin mulkin sojin Æasar don samo wani ÆwaÆÆwaran alÆawari.
Bayan wani taron sirri da malaman, jagoran tafiyar, Ustaz Abdullahi Bala-Lau ya ce Tinubu na neman a kauce wa amfani da Æarfi don warware rikicin, kuma a tabbatar an mayar da Nijar kan tafarkin tsarin mulki.
Ya ce Tinubu ya karÉi shawarwarinsu na a kauce wa amfani da Æarfin soja wajen kawo Æarshen duk wata taÆaddama, musamman ma a tsakanin maÆwabta da manyan Æawaye na tsawon lokaci.
A ranar Laraba ne, malaman addinin Musuluncin suka koma Nijar a karo na biyu, inda suka gana Shugaba Abdurahamane Tchiani da Firaminista Ali Lamine Zeine, kafin su dawo Abuja don yi wa Shugaba Tinubu bayani a kan matsayar da suka cimma.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ruwaito Sheikh Bala-Lau ya ce: “Wannan ce ta sa ya sake cewa mu koma Nijar don mu ci gaba da tattaunawa a ÆoÆarin ganin an mayar da Æasar kan tsarin dimokraÉiyya.
Ya kuma umarci mu sake tuna wa shugabannin sojin Nijar cewa akwai fa shawarar da Ecowas ta yanke game da juyin mulki”.
A cewarsa, kwalliya ta biya kuÉin sabulu a shiga tsakanin da malaman suka yi, abin da ya sa har shugabannin mulkin sojin suka karÉi masu shiga tsakani na Æungiyar Ecowas ÆarÆashin jagorancin Janar Abdulsalami Abubakar da Mai alfarma Sarkin Musulmi Abubakar Sa’ad III.
Shehin malamin ya ce za su koma Nijar ne don ci gaba da tattaunawa, don kuwa sun fahimci cewa jazaman yaÆi ya kasance zaÉi na Æarshe.
BBC Hausa
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.








