Home Labarai Tinubu ya bukaci  malamai su koma Nijar a karo na uku

Tinubu ya bukaci  malamai su koma Nijar a karo na uku

 

Shugaba Bola Tinubu ya umarci ayarin malaman addinin Musulunci da ke shiga tsakani a rikicin Jamhuriyar Nijar su koma wajen shugabannin mulkin sojin ƙasar don samo wani ƙwaƙƙwaran alƙawari.

Bayan wani taron sirri da malaman, jagoran tafiyar, Ustaz Abdullahi Bala-Lau ya ce Tinubu na neman a kauce wa amfani da ƙarfi don warware rikicin, kuma a tabbatar an mayar da Nijar kan tafarkin tsarin mulki.

Ya ce Tinubu ya karɓi shawarwarinsu na a kauce wa amfani da ƙarfin soja wajen kawo ƙarshen duk wata taƙaddama, musamman ma a tsakanin maƙwabta da manyan ƙawaye na tsawon lokaci.

A ranar Laraba ne, malaman addinin Musuluncin suka koma Nijar a karo na biyu, inda suka gana Shugaba Abdurahamane Tchiani da Firaminista Ali Lamine Zeine, kafin su dawo Abuja don yi wa Shugaba Tinubu bayani a kan matsayar da suka cimma.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ruwaito Sheikh Bala-Lau ya ce: “Wannan ce ta sa ya sake cewa mu koma Nijar don mu ci gaba da tattaunawa a Æ™oÆ™arin ganin an mayar da Æ™asar kan tsarin dimokraÉ—iyya.

Ya kuma umarci mu sake tuna wa shugabannin sojin Nijar cewa akwai fa shawarar da Ecowas ta yanke game da juyin mulki”.

A cewarsa, kwalliya ta biya kuÉ—in sabulu a shiga tsakanin da malaman suka yi, abin da ya sa har shugabannin mulkin sojin suka karÉ“i masu shiga tsakani na Æ™ungiyar Ecowas Æ™arÆ™ashin jagorancin Janar Abdulsalami Abubakar da Mai alfarma Sarkin Musulmi Abubakar Sa’ad III.

Shehin malamin ya ce za su koma Nijar ne don ci gaba da tattaunawa, don kuwa sun fahimci cewa jazaman yaƙi ya kasance zaɓi na ƙarshe.

BBC Hausa


Discover more from Albarka Radio

Subscribe to get the latest posts sent to your email.