Latest:
Labarai

An yi Fyade wa wata ƴar shekara 18 har lahira a Taraba

 

Wasu da ba a san ko su waye ba sun yi wa wata yarinya ‘yar shekara 18 mai suna Miss Wassa Joel Tuwa ‘yar Karamar Hukumar Yoro ta jihar Taraba fyade har lahira a hanyar wani daji da ke kauyen Rankabiri kusa da Jalingo babban birnin Jihar Taraba.

Wata majiyar daga dangin wacca abin ya shafa, Mista Ayuba Solomon Bissa ya shaida wa wakilinmu cewa an yi wa Mis Tuwa fyade tare da kashe ta yayin da aka jefa gawar a bayan wani dutse kusa da Jalingo.

A cewar Ayuba, marigayiyar ta bar gidansu da ke Jalingo zuwa Lankabirir, wani kauye kusa da yammacin ranar Asabar. Ta bi ta wata karamar hanyar kasuwa da ke kusa da Lankabiri don ta samu saukin tafiyar inda a nan ne suka tare suka yi mata fyade har ta mutu.

Ya kuma bayyana cewa binciken da likitocin suka gudanar ya nuna cewa an yi wa matar fyaden ne kafin daga bisani a kashe ta.

“A ranar Lahadi da safe ne wani karamin yaro da ke tallan itace ya gano gawar ta a gefen hanya, ya koma a guje ya sanar da iyayensa abin da ya gani, sai iyayen yaron da sauran mazauna wurin suka je wurin, suka gano gawarta a gefen hanya kusa da wani dutse.

Leadership Hausa

Leave a Reply