Skip to content
September 14, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Gwamnatin tarayya ta musanta zargin sasantawa da ƴan bindiga a Zamfara

September 26, 2023 2 minutes read

Ministan tsaron Najeriya, Muhammad Badaru Abubakar ya musanta zargin da gwamnan jihar Zamfara ya yi na cewa gwamnatin tarayya na ƙoƙarin sasantawa da ƴan bindiga.

A wata sanarwa da aka wallafa a shafin X na ma’aikatar tsaron Najeriya, ministan ya ce gwamnatin tarayya ba ta umurci wani ko wasu su tattauna da ƴan bindiga a madadinta ba.

Sanarwar ta kara da cewa gwamnatin Tinubu na aiki domin ceto sauran daliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau, waɗanda aka sace a ranar Juma’a.

A cewar Badaru a yanzu haka sojoji sun ceto dalibai 13 da kuma leburori uku daga cikin mutanen da ƴan bindiga ke garkuwa da su.

A ranar Litinin ne gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya fitar da wata sanarwa inda ya zargi Gwamnatin Tarayya da yin tattaunawar sirri da ƴan fashin daji a jihar Zamfara ba tare da sanin gwamnatin jihar ba.

Sai dai da yammacin Litinin, wata sanarwa daga ofishin ministan yaɗa labaru da wayar da kan al’umma na Najeriya ta musanta batun, tare da zargin gwamnan na jihar Zamfara da ƙoƙarin siyasantar da batun tsaro.

Sai dai duk da haka gwamnan, ta hannun mai taimaka masa kan yaɗa labaru da hulɗa da jama’a ya sake fitar da wata sanarwar a ranar Talata inda ya ce gwamnatin jihar tana da shaidu na irin tattaunawar da ta gudana tsakanin jami’an gwamnatin tarayya da ƴan fashin dajin.

Masana tsaro na kallon musayar kalaman tsakanin ɓangarorin biyu a matsayin wani abu da ka iya yin cikas ga ƙoƙarin gwamnati na yaƙi da ayyukan ƴan fashin dajin a yankin na arewa maso yammacin Najeriya.

BBC Hausa

Tags: Bello Matawalle Gwamna Dauda Lawal Muhammad Badaru Zamfara

Post navigation

Previous: Mun nemi ƙarin bayani daga Gwamnatin Tarayya kan zaman sirri na sulhu da wasu jami’anta suke jagoranta a Zamfara – Dauda
Next: DSS Sun Kama Babban Editan jaridar Al-Mizan

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.