Skip to content
September 20, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Sojojin Najeriya sun hallaka ƴan bindiga sama da 100

October 12, 2023 2 minutes read

Rundunar sojin Najeriya ta ce kashe yan bindiga fiye da 100 a karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara da ke Arewa Maso Yammacin kasar.

Wannan na zuwa ne bayan babban hafsan sojin Najeriyar, Janar Christopher Musa ya umarci dakarun su bi ƴan bindigar har maɓoyar su don kawar da su.

Rahotanni sun ce sashin sojin sama na rundunar Operation Hadarin Daji ce ta yi wannan aiki, bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa yan bindigar suna kan hanyar su ta kai hari a wani kauye.

Majiya daga rundunar sojin ta ce dakarun rundunar sun yi amfani da jirgin sama wajen kashe yan bindigar da ke tafiya cikin ayari da mashinan su, a yankin Dansadau na karamar hukumar Maru.

Akwai kuma raunata wasu yan bindigar da dama a yayin arangamar da suka yi da sojojin Najeriyar.

Wannan na zuwa ne ƙasa da kwana guda bayan da babban hafsan sojin Najeriyar, Janar Christopher Musa ya umarci dakarun nasa su gaggauta kawar da ƴan bindigar da ke addabar al’ummar ƙasar, musamman a jihohin Arewa Maso Yamma.

A lokacin wata ziyara da ya kai wa dakarun rundunar sojin Najeriya da ke yaki da ƙungiyar Boko Haram ne Janar Christopher Musa ya umarci dakarun su daina jira sai yan bindigar da sauran masu dauke da makamai sun kawo masu hari kafin su dauki mataki, inda ya bayar da umarnin bin masu laifin har mafakar su domin kawar da su.

“Kada ku kwanta a sansaninku kuna jira su zo, ku tabbata kun zakulo makiya da ke addabar mutanen mu ku kashe su. Abin da ya fi dacewa shi ne ku same su har maboyar su, kuma ku kawar da su’’ inji Janar Musa.

A lokacin waccan ziyara dai babban hafsan sojin Najeriyar ya isar da sakon shugaban kasar, Bola Tinubu wanda ya ce yana sane da sadaukarwar da dakarun sojin ke yi wajen yaki da yan bindiga da sauran masu tayar da kayar baya, da kuma neman zaunar da kasar lafiya.

BBC Hausa

Tags: Sojojin Najeriya ƴan bindiga Zamfara

Post navigation

Previous: Wike zai kulla alaka da Isra’ila don samar da tsaro a Abuja
Next: Mutum 1,715 ƴan bindiga suka kashe cikin wata uku a Najeriya, cewar wani Rahoto

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.