Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana sunan Dr. Olayemi Michael Cardoso a matsayin sabon gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) na tsawon shekara biyar, da zarar Majalisar Dattijan Æasar ta amince da shi.
Wannan bayani na Æunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Æasar, Ajuri Ngelale ya fitar, yau Juma’a.
Bayanin ya ce shugaban Æasar ya Éauki matakin ne bisa dogaro da sashe na 8 (1) na dokar Babban Bankin Najeriya ta 2007, wadda ta bai wa shugaban Æasar karfin ikon naÉa shugaba da mataimaka huÉu na Babban Bankin.
Sanarwar ta kuma bayyana sunayen wasu mutane huÉu da shugaban ya amince da su domin naÉawa a matsayin mataimakan gwamnan babban bankin na Najeriya.
Mataimakan su ne:
(1) Mrs. Emem Nnana Usoro
(2) Mr. Muhammad Sani Abdullahi Dattijo
(3) Mr. Philip Ikeazor
(4) Dr. Bala M. Bello
Shugaban ya buÆaci waÉanda aka naÉan su mayar da hankali wajen aiwatar da muhimman sauye-sauyen da aka Éullo da su a bankin a ÆoÆarin gwamnatinsa na sake fasalin tattalin arziÆin Æasar.
A watan Yunin wannan shekara ne shugaban Æasar ya dakatar da gwamnan babban bankin Æasar, Godwin Emefiele.
Wata sanarwa da ta fito daga ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayyar Æasar ta ce an dakatar da Emefiele ne ne domin gudanar da bincike da kuma kasancewa wani Éangare na ÆoÆarin sauya fasalin harkokin kuÉi a Æasar.
Kwanaki kaÉan bayan dakatar da shi ne rundunar tsaron ciki ta Æasar, DSS ta tabbatar da kamawa tare da tsare tsohon gwamnan babban bankin.
DSS Éin ta kuma gurfanar da Emefiele a gaban kotu bisa tuhumar sa da laifuka daban-daban.
BBC Hausa
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.









