Daga Zainab Faruk
Uwargidar Gwamnan Jihar Bauchi, Hajiya Aishatu Bala Abdulkadir Muhammad, ta kai ziyarar taâaziyya ga iyalan marigayi Alhaji Abubakar Jafaru Ilelah, tsohon Hadimin Gwamna na Musamman kan Wayar da Kan Jamaâa kuma Babban Mai Gabatar da Shirye-shiryen Gwamnatin Jihar Bauchi, wanda ya rasu kwanan nan.
A yayin jawabin nata ga iyalan mamacin, Hajiya Aishatu ta mika taâaziyya gare su, musamman ga mata da âyaâyan mamacin da sauran dangi da abokan arziki. Ta bayyana mutuwar a matsayin jarabawa daga Allah da kuma tunatarwa ga kowa da kowa game da cewa duniya ba wajen zama ba ne.
âInna lillahi wa inna ilaihi rajiâun. Muna godewa Allah a kan kowanne hali da muka tsinci kanmu a ciki, domin mu bayi ne, kuma Allah yana gwada bayinsa da cuta, talauci ko mutuwa,â in ji ta.
Ta bukaci âyaâyan mamacin da su dage sannan su kyautata halayensu, su kasance masu neman ilimi da yin adduâoâi, inda ta bayyana cewa daya daga cikin mafi kyawun abin da uba zai bari a duniya shi ne âyaâya nagari da ke yawan yi masa adduâa. âHakkin mahaifinku yanzu ya dawo kan ku da mahaifiyarku. Ya wajaba ku kasance masu hankali, masu adduâa da kuma neman ilimi,â ta shawarce su.
Da take tuna halayen kirkin mamacin, Hajiya Aishatu ta yaba da yadda marigayin ke kasancewa cikin natsuwa da murmushi a koda yaushe, ba tare da nuna bacin rai ba. Ta ce: âMutum ne da a ko yaushe idan ka ganshi yana cikin faraâa, ba a taba ganinsa cikin bacin rai. Wannan shi ne irin kyakkyawar gadon da ya bari.â
Ta kuma bukaci âyan uwansa da su ci gaba da hada kai da zama tare da juna cikin jituwa, musamman maza daga cikin âyaâyan mamacin da yanzu ke da nauyin kula da iyali. Sai dai ta jaddada cewa hakan ba ya nufin mata ba su da rawar takawa wajen neman ilimi ko sanaâa. âAllah bai ce mata kada su nemi ilimi ko sanaâa ba. Amma dai maza ne aka dora da alhakin kulawa da su.â
A karshe, ta juyo ga uwargidan mamacin, inda ta bayyana cewa nauyin da ke kanta yanzu ya ninka, kuma ta roki Allah ya ba ta ikon kula da âyaâyanta cikin tarbiyya da tsoron Allah. âAllah ya bude maki kofa daga cikin taskokinsa, ya ba ki ikon tarbiyyar âyaâyanki yadda ya dace,â in ji ta.
Hajiya Aishatu ta kammala ziyarar da adduâoâi na musamman ga marigayi Alhaji Jafaru Ilelah, inda ta roki Allah ya gafarta masa, ya karbi ibadunsa ya masa rahama, ya azurta iyalansa da zumunci da karfin guiwa da kuma zaman lafiya.
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.









