Ana fargabar cewa wasu âyan taâadda da ake kyautata zaton âyan bindiga ne sun kashe wasu maâaurata da wani malamin makaranta a kauyen Maro da ke Karamar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna.
Lamarin kamar yadda wakilinmu ya ruwaito, ya jefa mazauna yankin na Unguwar Dorawar Bakhira cikin firgici, yayin da malamin da lamarin ya rutsa da shi mai suna Mista Sunday Akorh, ya kasance malamin firamare daya tilo a kauyen.
Mazauna sun shaida wa Aminiya cewa, babu wanda aka samu rahoton cewa an yi awon gaba da shi a yayin harin da âyan taâaddan suka kai da misalin karfe 1:30 na daren Asabar wayewar garin Lahadi.
Wani mazauni kuma jagoran alâumma a yankin, Maigari Ben, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin zantarwarsa da Aminiya a wannan Lahadin.
âSun kashe wani mutum da matarsa da wani malamin firamare mai suna Mista Sunday Akorh dan asalin Jihar Benuwai.
âMalamin shi kadai ne yake koyarwa a wata makarantar firamare a wannan kauyen. Sai dai babu wanda aka yi garkuwa da shi,â a cewarsa.
Sai dai kokarin da wakilinmu ya yi domin jin ta bakin jamiâin hulda da rundunar âyan sandan Jihar Kaduna, ASP Manir Hassan ya ci tura a yayin da ba a same shi a wayarsa ba, sannan kuma bai bayar da amsar sakon kar ta kwana da aka tura masa ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.
Jaridar Aminiya
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.









