Skip to content
September 13, 2026
  • About Us
  • Contact Us
  • Personal Information Usage Disclosure
  • Privacy Policy
Albarka Radio

Albarka Radio

Official Website of Albarka Radio, Bauchi.

Primary Menu
  • Home
  • Breaking News
  • Education
  • Health
  • National News
  • Latest News
  • Politics
  • Sports
  • Featured
Light/Dark Button
Listen Live
  • Labarai

Ƴan Bindiga Sunyi Ajalin Ma’aurata Da Malamin Firamare A Kaduna

October 29, 2023 2 minutes read

 

Ana fargabar cewa wasu ’yan ta’adda da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne sun kashe wasu ma’aurata da wani malamin makaranta a kauyen Maro da ke Karamar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna.

Lamarin kamar yadda wakilinmu ya ruwaito, ya jefa mazauna yankin na Unguwar Dorawar Bakhira cikin firgici, yayin da malamin da lamarin ya rutsa da shi mai suna Mista Sunday Akorh, ya kasance malamin firamare daya tilo a kauyen.

Mazauna sun shaida wa Aminiya cewa, babu wanda aka samu rahoton cewa an yi awon gaba da shi a yayin harin da ’yan ta’addan suka kai da misalin karfe 1:30 na daren Asabar wayewar garin Lahadi.

Wani mazauni kuma jagoran al’umma a yankin, Maigari Ben, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin zantarwarsa da Aminiya a wannan Lahadin.

“Sun kashe wani mutum da matarsa da wani malamin firamare mai suna Mista Sunday Akorh dan asalin Jihar Benuwai.

“Malamin shi kadai ne yake koyarwa a wata makarantar firamare a wannan kauyen. Sai dai babu wanda aka yi garkuwa da shi,” a cewarsa.

Sai dai kokarin da wakilinmu ya yi domin jin ta bakin jami’in hulda da rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Manir Hassan ya ci tura a yayin da ba a same shi a wayarsa ba, sannan kuma bai bayar da amsar sakon kar ta kwana da aka tura masa ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Jaridar Aminiya

Tags: Kaduna ƴan bindiga Zaria

Post navigation

Previous: Bauchi healthcare sector to benefit from World Bank PHC intervention.
Next: Ana yunkurin tsige Gwamnan jihar Rivers 

Related Stories

  • Labarai

Sakon Sakatare Janar Na MDD Na Murnar Fara Azumin Ramadan 2026

February 17, 2026
  • Labarai

Fiye da Mata 100 Sun Kammala Samun Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani a Bauchi Karkashin Shirin Renewed Hope Initiative

July 30, 2025
  • Labarai

“Jami’ar PDP ba ta da alkibla a jihar Bauchi” In ji wani jigo a jam’iyyar APC

July 30, 2025

You May Have Missed

  • News

Nigeria Moves to Unlock $1.2bn ECOWAS Trade Market, Urges Nigerian Businesses to Conquer West African Markets

September 5, 2026
  • Opinion

Nigeria Rejoins World Energy Council – Wunti Takes the Helm

August 8, 2026
  • News

Fathers’ Forum Sparks Change in Bauchi, Men Rally Behind Girls’ Education

June 8, 2026
  • News

Bauchi Mothers Drive Grassroots Push for Girls’ Education and Empowerment

June 8, 2026
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy
Copyright © 2026 Albarka Radio, All rights reserved. | ReviewNews by AF themes.