Wasu da ake zargin âyan bindiga ne, sun kashe mutum uku wasu sun samu raunuka a wani sabon harin da suka kai a yankin Soro da ke a karamar hukumar Binji, a jihar Sakkwato.Â
Kakakin runudanar âyansandan jihar, Ahmad Rufai ne, ya tabbatar da kai harin wanda ya ce, ya auku ne a ranar Litinin.
A cewar Ahmad, âyan bindigar sun kaddamar da harin ne a yankin Soro, amma jamiâan rundunar tare da taimakon jamiâan soji, sun samu nasarar dakile harin âyan bindigar.
Kazalika ya ce, âyan bindigar sun kuma banka wa wasu gidaje wuta, wanda sakamakon hakan mutum uku suka rasu, wasu kuma suka samu raunuka.
Wasu majiyoyi a yankin sun bayyana cewa, maharan sun sace mutane da dama tare da kuma banka wa wasu gidaje wuta.
Bugu da kari, wasu mazauna yankin sun bayyana cewa, wasu âyan sintiri a yankin ne suka dakile harin âyan bindigar, wanda daga baya kwamishinan âyansandan jihar ya shiga tsakani domin tattaunawa da mazauna yankin.
Jaridar leadership
Discover more from Albarka Radio
Subscribe to get the latest posts sent to your email.









